Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Jihar Niger

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Jihar Niger

Akalla fararen hula mutum 43 ne suka mutu wanda suka hadar da sojojin 30 da ‘yan sandan kwantar da tarzo 7 sakamakon harin ‘yan bindiga a wani wurin hakar ma’adanai  a karamar hukumar Shiroro dake jihar Nijer, kamar yadda wata majiya ta shaida mana.

A yayin da gwamnatin jihar ta Niger ke tabbatar da faruwar harin, ta bayyana cewa bata kai ga gano adadin wadanda harin ya rutsa dasu ba.

Mazauna yakin sun bayyana cewa jami’an Bincike sun gano gawarwakin sojoji da Jami’an ‘yan sandan 37 yashe a cikin daji ranar Alhamis, gami da gawarwakn fararen hula 6 duk a cikin dajin.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da ‘yan Nijeriya da ‘yan kasar Sin (Chaina) da dama a yayin harin da suka kai wajen hakar ma’adanan a ranar laraba.

Yusuf Kokki, wanda gudana ne cikin shuwagabannin kungiyar Matasan Shiroro, ta cikin wata sanarwa da ya aikewa manema labarai yace mazauna wurin sun shaida harin maharan dauke da muggan makamai.

Ya tabbatar da cewa lamarin ya faru ne yayin da ‘yan bindigar suka yiwa wurin hakar ma’adanan tsinke, nan suka fara harbi kan mai uwa da wabi akan ma’aikatan da masu tsaron lafiyar su.

Ya ce mazauna yankin zasu zakulo Karin wasu gawarwakin a aikin da suke cigaba da yi na nemo wadanda harin ya rutsa dasu.

Yace jami’an ‘yan sandan kwantar da tarzoma 7 sun mutu da wasu Karin fararen hula guda 6 a wajen hakar ma’adanan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp