Home Labarai ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Jihar Niger

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Jihar Niger

Akalla fararen hula mutum 43 ne suka mutu wanda suka hadar da sojojin 30 da ‘yan sandan kwantar da tarzo 7 sakamakon harin ‘yan bindiga a wani wurin hakar ma’adanai  a karamar hukumar Shiroro dake jihar Nijer, kamar yadda wata majiya ta shaida mana.

A yayin da gwamnatin jihar ta Niger ke tabbatar da faruwar harin, ta bayyana cewa bata kai ga gano adadin wadanda harin ya rutsa dasu ba.

Mazauna yakin sun bayyana cewa jami’an Bincike sun gano gawarwakin sojoji da Jami’an ‘yan sandan 37 yashe a cikin daji ranar Alhamis, gami da gawarwakn fararen hula 6 duk a cikin dajin.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da ‘yan Nijeriya da ‘yan kasar Sin (Chaina) da dama a yayin harin da suka kai wajen hakar ma’adanan a ranar laraba.

Yusuf Kokki, wanda gudana ne cikin shuwagabannin kungiyar Matasan Shiroro, ta cikin wata sanarwa da ya aikewa manema labarai yace mazauna wurin sun shaida harin maharan dauke da muggan makamai.

Ya tabbatar da cewa lamarin ya faru ne yayin da ‘yan bindigar suka yiwa wurin hakar ma’adanan tsinke, nan suka fara harbi kan mai uwa da wabi akan ma’aikatan da masu tsaron lafiyar su.

Ya ce mazauna yankin zasu zakulo Karin wasu gawarwakin a aikin da suke cigaba da yi na nemo wadanda harin ya rutsa dasu.

Yace jami’an ‘yan sandan kwantar da tarzoma 7 sun mutu da wasu Karin fararen hula guda 6 a wajen hakar ma’adanan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp