Home Labarai Hukumar ICPC Ta Gurfanar Da Mataimakin Kwamandan NSCDC Kan Badakalar N26.7m

Hukumar ICPC Ta Gurfanar Da Mataimakin Kwamandan NSCDC Kan Badakalar N26.7m

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ta ICPC ta gurfanar da mataimakin kwamandan hukumar dake bada kariya ga fararen hula ta Civil Defence Mr Boutidem Akpan gaban kotu kan zarginsa da badakalar kudaden da suka kai naira miliyan 26 da dubu dari 655.
An gurfanar da Mr Akpan gaban mai shari’a V. S. Gaba na babbar kotun tarayya dake Kwali a birnin Abuja ne bisa tuhumarsa da laifuffuka 17 dake da jibi da almundahana da dukiyar kasa, da ya hadar da amfani da sunan kamfaninsa wajen damfara.
Cikin takardar tuhumar dai ta nuna ana zarginsa da amfani da kujerarsa wajen yaudarar wasu mutane ta hanyar karbar kudi daga hannunsu da sunan hukumar, yana mai cewa hukumar ce za ta raba musu filaye a yankin Karshi da Sabon Lugbe da kan titin Filin jirgi da kuma wasu filaye a jihar Nassarawa, wanda kuma kawo yanzu ba a bas u filayen ba.
Hukuar ICPC dai ta shaidawa kotu cewa ya aikata laifukan ne a tsakanin shekarun 2010 zuwa 2015 kuma laifukan sun saba da sashi na 19 da 26 karamin sashi na 1 sakin layi na 3 na kundin dokokin hukumar na shekarar 2000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp