Home Labarai Hukumar ICPC Ta Gurfanar Da Mataimakin Kwamandan NSCDC Kan Badakalar N26.7m

Hukumar ICPC Ta Gurfanar Da Mataimakin Kwamandan NSCDC Kan Badakalar N26.7m

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ta ICPC ta gurfanar da mataimakin kwamandan hukumar dake bada kariya ga fararen hula ta Civil Defence Mr Boutidem Akpan gaban kotu kan zarginsa da badakalar kudaden da suka kai naira miliyan 26 da dubu dari 655.
An gurfanar da Mr Akpan gaban mai shari’a V. S. Gaba na babbar kotun tarayya dake Kwali a birnin Abuja ne bisa tuhumarsa da laifuffuka 17 dake da jibi da almundahana da dukiyar kasa, da ya hadar da amfani da sunan kamfaninsa wajen damfara.
Cikin takardar tuhumar dai ta nuna ana zarginsa da amfani da kujerarsa wajen yaudarar wasu mutane ta hanyar karbar kudi daga hannunsu da sunan hukumar, yana mai cewa hukumar ce za ta raba musu filaye a yankin Karshi da Sabon Lugbe da kan titin Filin jirgi da kuma wasu filaye a jihar Nassarawa, wanda kuma kawo yanzu ba a bas u filayen ba.
Hukuar ICPC dai ta shaidawa kotu cewa ya aikata laifukan ne a tsakanin shekarun 2010 zuwa 2015 kuma laifukan sun saba da sashi na 19 da 26 karamin sashi na 1 sakin layi na 3 na kundin dokokin hukumar na shekarar 2000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp