Home Labarai Hukumar ICPC Ta Gurfanar Da Mataimakin Kwamandan NSCDC Kan Badakalar N26.7m

Hukumar ICPC Ta Gurfanar Da Mataimakin Kwamandan NSCDC Kan Badakalar N26.7m

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ta ICPC ta gurfanar da mataimakin kwamandan hukumar dake bada kariya ga fararen hula ta Civil Defence Mr Boutidem Akpan gaban kotu kan zarginsa da badakalar kudaden da suka kai naira miliyan 26 da dubu dari 655.
An gurfanar da Mr Akpan gaban mai shari’a V. S. Gaba na babbar kotun tarayya dake Kwali a birnin Abuja ne bisa tuhumarsa da laifuffuka 17 dake da jibi da almundahana da dukiyar kasa, da ya hadar da amfani da sunan kamfaninsa wajen damfara.
Cikin takardar tuhumar dai ta nuna ana zarginsa da amfani da kujerarsa wajen yaudarar wasu mutane ta hanyar karbar kudi daga hannunsu da sunan hukumar, yana mai cewa hukumar ce za ta raba musu filaye a yankin Karshi da Sabon Lugbe da kan titin Filin jirgi da kuma wasu filaye a jihar Nassarawa, wanda kuma kawo yanzu ba a bas u filayen ba.
Hukuar ICPC dai ta shaidawa kotu cewa ya aikata laifukan ne a tsakanin shekarun 2010 zuwa 2015 kuma laifukan sun saba da sashi na 19 da 26 karamin sashi na 1 sakin layi na 3 na kundin dokokin hukumar na shekarar 2000.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp