Home Taska An Cire Mukaddashin Babban Akantan Najeriya, Mr Chukwuyere Anamekwe

An Cire Mukaddashin Babban Akantan Najeriya, Mr Chukwuyere Anamekwe

An Cire Mukaddashin Babban Akantan Najeriya, Mr Chukwuyere Anamekwe

 

Gwamnatin Najeriya ta cire mukaddashin babban akantan kasar Mr. Chukwuyere N. Anamekwe inda aka maye gurbinsa da Mr. Okolieaboh Ezeoke Sylvis, wanda tsohon darekta ne a tsarin asusun gwamnati na bai-daya, wato, TSA (Treasury Single Account).

Rahotanni na cewa an maye gurbin mai rikon mukamin na Akanta-Janar din ne saboda hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasar zagon-kasa, EFCC, na bincike a kansa.

Haka kuwa ana cewa gwamnatiun ba ta ji dadin wasu kalamai da ya yi ba inda ya ce, Najeriya na ranto kudi domin ta biya albashi.

Anamekwe wanda aka nada shi a wannan matsayi na rikon-kwarya a ranar 22 ga watan Mayu bayan da hukumar EFCC ta kama Babban Akantan kasar, Ahmed Idris bisa zargin almundahana da naira biliyan 80, ya yi kalaman cin bashin ne, a ranar 14 ga watan Yuni, na 2022, kuma kwana bakwai daga nan aka cire shi.

Mista. Sylva, wanda ke zaman mukaddashin Babban Akantan a yanzu, rahotanni na nuni da cewa zai yi ritaya a cikin watanni uku na farkon shekara mai zuwa, 2023.

Tuni dai gwamnatin tarayyar Najeriyar ta kaddamar da neman wanda za ta nada a matsayin sabon Babban Akantan, kamar yadda bayanai ke nunawa.

Jaridar The Nation ta Najeriyar ta ruwaito cewa duk wani kokari da ta yi na neman gaskiyar kalaman da Anamekwe ya yi cewa gwamnati na ciyo bashi ta biya albashi, ya ci tura.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp