Home Labarai Yadda Firsunoni 879 Suka Gudu Daga Gidan Gyaran Hali a Nijeriya

Yadda Firsunoni 879 Suka Gudu Daga Gidan Gyaran Hali a Nijeriya

Hukumar dake lura da Gidajen Gyaran hali ta Nijeriya ta tabbata da cewa DCP Abba Kyari da wasu wadanda ake basu kula ta musamman a gidan gyaran hali na kuje dake birnin tarayya Abuja basu tsere ba.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin hukumar CSPC Umar Abubakar AICMC, ANIPR., wadda aka aikewa PRNigeria, amadadin babban kwantirolan hukumar.

Wannan dai na zuwa ne tun bayan wani hari da ake zargin mayakan kungiyar tada kayar baya na boko haram sun kai gidan gyaran hali na Kuje dake birnin tarayya Abuja,

Sanarwar tace fursunoni 879 ne suka tsere daga wurin a lokacin da maharani suka musu dirar mikiya, said ai ya zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto an sami nasarar kamo 551 inda kuma 443 suka dawo don radin kansu, baya ga fursunoni 4 da suka rasa rayukan su, in da fursunoni 16 suka sami muggan raunika kuma yanzu haka suna karbar kulawa ta musamman, inda tace ana kuma ci gaba da kokarin nemo sauran firsunonin.

Haka kuma hukumar ttace ta girki jami’an ta na sashen bayanai (CIMS) tare da hadin gwuiwar jami’an hukumar samar da katin shaidar zama dan kasa (NIMC) domin bin diddigin duk fursunonin da suka gudau tare dadawo da su gidan gyaran halin.

Sannan kuma sanar tace hukumar na amfani da wannan dama wajen tabbatarwa da jama’a cewa DCP Abba Kyari da sauran manyan jami’an tsaro da ake tsare da su a wajen basu gudu ba, a halin yanzu suna hannun hukumar cikin koshin lafiya.

Idan dai za’a iya tunawa, tun bayan harin da aka kai cibiyar gyaran hallin ta Agbolongo dake jihar Oyo, ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, ya gana da shuwagabannin hukumomin tsaro dake karkashin sa, domin yin hadin gwuiwar jami’an da suka kunshi na hukumar Gyaran Hali ta kasar, hukumar dake lura da shige ta fice da kuma hukumar tsaron ta civil Defence, hukumar tsaro ta Farin kaya DSS, da kuma rundunar sojojin kasar, domin dakile ci gaba da samun irin wannan matsala.

Sanarwa ta kara da tabbatar da cewa a yayin artabun da jami’an dake tsaron gidan gyaran halin sun sami nasarar hallaka da dama cikin su, yayin da wasu suka tsere da raunin harbin bindiga.

Daga bisani hukumar ta bukaci Asibitoci da sauran cibiyoyin kiwon lafiya da likitoci su kai rahoton duk wanda ya zo wurin su don jinyar raunin Harbin bindiga ga hukumomin tsaro mafi kusa.

Sanarwa ta Ambato babban kwantirolan hukumar ta gyaran Hali Haliru Nababa FICMC, mni na yabawa da kokarin sauran jami’an tsaron bisa kai daukin gaggawa akan lokaci, ya kuma yi kira ga jama’a da su taimaka da sahihan bayanan da zasu taimake su wajen kame sauran firsunonin da suka tsere.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp