Home Labarai An Sami Bullar Kyandar Biri A Jihar Katsina

An Sami Bullar Kyandar Biri A Jihar Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da bullar cutar Kyandar biri karon farko a jihar, kuma sun masa magani sun sallame shi.

Kwamishinan lafiya na jihar Yakubu Danja, ne ya tabbatar da bullar cutar yayin da yake gabatar da fara rabon magungu kyauta a kananan hukumomi 34 dake fadin jihar.

Yace sun sami mutum 15 da ake zargin suna dauke da cutar kuma an dauki samfurin gwajin zuwa birnin tarayya Abuja, wanda yanzu haka ana sauraren sakamako.

Danja ya kuma bayyana cewa za’a raba magungunan kyauta ga cibiyoyin bada maganin a jihar, kana Gwamnatin ta himmatu wajen wayar da kan dukkan kungiyoyin bada Agajin gaggawa domin dakile yaduwar Cutar.

Ya kara da cewa daga cikin magungunan da aka raba domin dakile yaduwar cututtuka har da maganin cutar kwalara da sauran cutattukan dake da alaka da zuwan yanayin damuna.

Daga bisani kwamishinan ya zaga cibiyar bayar da Agajin gaggawa inda ya mika na’urar Firinji guda140 domin Ajje alluran, ya kuma tabbatar da cewa hukumar lafiya matakin farko ce ta bayar da su kyauta.

HealthDigest

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp