Home Labarai An Sami Bullar Kyandar Biri A Jihar Katsina

An Sami Bullar Kyandar Biri A Jihar Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina ta sanar da bullar cutar Kyandar biri karon farko a jihar, kuma sun masa magani sun sallame shi.

Kwamishinan lafiya na jihar Yakubu Danja, ne ya tabbatar da bullar cutar yayin da yake gabatar da fara rabon magungu kyauta a kananan hukumomi 34 dake fadin jihar.

Yace sun sami mutum 15 da ake zargin suna dauke da cutar kuma an dauki samfurin gwajin zuwa birnin tarayya Abuja, wanda yanzu haka ana sauraren sakamako.

Danja ya kuma bayyana cewa za’a raba magungunan kyauta ga cibiyoyin bada maganin a jihar, kana Gwamnatin ta himmatu wajen wayar da kan dukkan kungiyoyin bada Agajin gaggawa domin dakile yaduwar Cutar.

Ya kara da cewa daga cikin magungunan da aka raba domin dakile yaduwar cututtuka har da maganin cutar kwalara da sauran cutattukan dake da alaka da zuwan yanayin damuna.

Daga bisani kwamishinan ya zaga cibiyar bayar da Agajin gaggawa inda ya mika na’urar Firinji guda140 domin Ajje alluran, ya kuma tabbatar da cewa hukumar lafiya matakin farko ce ta bayar da su kyauta.

HealthDigest

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp