Home Labarai Gwamnatin Nijeriya Ta Dora Alhakin Matsalolin Jigilar Aikin Hajjin Bana Kan Kamfanonin...

Gwamnatin Nijeriya Ta Dora Alhakin Matsalolin Jigilar Aikin Hajjin Bana Kan Kamfanonin Jiragen Sama

Hukumar kula da aikin Hajji ta Najeriya (NAHCON) ta Nemi afuwar Maniyatan kasar na bana dangane da wahalhalun da suka Sha yayin jigilar maniyatan daga kasar zuwa kasa mai tsarki domin gudanar da ibadar aikin Hajjin bana.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da jami’ar yada labaran hukumar NAHCON Fatima Sanda Usara ta fitar tace Hukumar ta kuma Nemi afuwar gwamnatin tarayyar kasar, da hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi, masu kamfanonin jirgin yawo, sauran jama’a kan duk abubuwa marasa dadi da suka faru a makonnin da suka gabata.

Abin takaicin shi ne, duk da kokarin da aka yi na jigilar dukkan maniyyatan Najeriya da ke da niyyar zuwa kasar Saudiyya don gudanar da aikin Hajjin 2022, NAHCON ta gaza wajen sauke wannan nauyi, musamman dalilin koma bayan da aka samu a karshen makon da ya gabata, wanda ya kawo cikas ga shirinta na kammala jigilar maniyyatan zuwa ranar 27 ga watan Yuni na wannan shekara.

“Sai dai abin takaicin shi ne, yadda kamfanonin jirgin da muka zaba kuma suka bamu tabbacin zasu iya wannan aikin Amma su ne silar duk wadannan matsaloli da muka samu na kasa kammala jigilar dukkanin maniyatan kasar nan zuwa kasa mai tsarki.

Musamman, wadannan adadin maniyyatan da abin ya shafa ba sune muka gaza kaisu kasar saudiyya har lokacin rufe filin jirgi sama na jidda ,wanda hakan ya tabbatar da cewa sun rasa aikin Hajjin na bana. akwai maniyatan tara (9) daga jihar Bauchi; maniyatan 91 daga jihar Filato; Maniyata 700 ne daga jihar Kano da kuma mahajjata kimanin 750 daga bangaren masu bin jirgin yawo.

Sanarwar tace Hukumar ta ba da tabbacin cewa za a mayar wa dukkan maniyyatan da abin ya shafa kudin aikin Hajjinsu yayin da za ta yi kokarin gyara matsalolin da a nan gaba.

NAHCON ta koyi darussa da dama kuma ta kuduri aniyar ganin hakan bata a sake faruwa ba, Hukumar bata da kalmomin da zata yi amfani dasu wajen hakurkurtar da yan Nigeria musamman wadanda suka kudiri aniyar aikin Hajjin sakamakon mawuyacin halin da suka tsinci kansu a ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp