Home Labarai Bayan Jaridar PRNigeria Ta Gudanar Da Binciken A Asibitocin Kano Wata Gidauniya...

Bayan Jaridar PRNigeria Ta Gudanar Da Binciken A Asibitocin Kano Wata Gidauniya Ta Bada Injin Wankin Koda Ga Asibiti Guda A Jihar.

Wata gidauniya mai lakabin Gidauniyar dashen Koda, guda cikin kungiyoyi masu zaman kansu (NGO’s) ta bayar da tallafin kayan aikin dashen koda ga asibitin kwararru na Muhammad Abdullahi Wase da ke jihar Kano a Arewacin Nijeriya.

Wani bincike na PRNigeria na baya-bayan nan ya nuna yadda rayuwar masu fama da ciwon koda da dama a Kano ke dogara da injinan wankin kodar koda 12 kacal a manyan cibiyoyin kiwon lafiya guda biyu da suka hadar da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) da Asibitin kwararru na Abdullahi Wase.

A Asibitin kwararru na Abdullahi Wase a kalla majinyata dake da nasaba da koda, 160 ke ziyartar asibitin duk mako, haka akan sami sabbin masu kamuwa daga cutar mutum 15 dake zuwa duk makon.

Yayin da a Asibitin koyarwa na Aminu Kano akan sami majinyata kusan 70 a duk mako dake zuwa domin wankin kodar. Amma akalla ana ganin masu fama da cutar mutum 40, baya ga yadda da dama ke zaman jira.

Duk da tsadar wankin na koda, wasu daga cikin injinan wankin basa aiki yadda ya kamata.

Da yake jawabi a yayin mika kayayyakin aikin ga asibitin shugaban gidauniyar dashen kodar, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya ce sun dauki wannan mataki ne domin rage radadi gami da wahalhalun da masu fama da lulurar ke fuskanta.

Ya kara da cewa sun dauki matakin tallafawa Asibitin na Abdullahi Wase ne sakamakon kokarin sa rage farashin kudin wankin koda ga masu fama da lalurar.

“Mun kashe sama da naira dubu dari biyar domin samar da kayan aikin wankin koda, don haka muna kira ga wasu kungiyoyi da masu hannun da shuni da suyi koyi da wannan abun Alkhari.

A nata jawabin, tsohuwar Ministar ilimi ta Nijeriya, Farfesa Rukayya Ahmad Rufa’I, wacce mamba ce a gidauniyar ta yi kira ga gwamnatin Jihar Kano da ta gaggauta daukar matakai domin magance kalubalen da asibitin ke fuskanta.

Babban Daraktan asibitin wanda ya sami wakilci Dr. Bashir Garba Ahmad ya yaba da irin hangen nesa da jajircewa da wannan gidauniya ta yi wajen rage radadin ga masu fama da lalurar.

Ya kara da cewa Asibitin na fuskantar kalubale masu tarin yawa, musamman na kayan da suka jibanci ayyukan lura da masu famada lalura koda, wanda ke bukatar gwamnatin jihar kano da masu ruwa da tsaki su gaggauta daukar mataki.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp