Home Labarai Bayan Jaridar PRNigeria Ta Gudanar Da Binciken A Asibitocin Kano Wata Gidauniya...

Bayan Jaridar PRNigeria Ta Gudanar Da Binciken A Asibitocin Kano Wata Gidauniya Ta Bada Injin Wankin Koda Ga Asibiti Guda A Jihar.

Wata gidauniya mai lakabin Gidauniyar dashen Koda, guda cikin kungiyoyi masu zaman kansu (NGO’s) ta bayar da tallafin kayan aikin dashen koda ga asibitin kwararru na Muhammad Abdullahi Wase da ke jihar Kano a Arewacin Nijeriya.

Wani bincike na PRNigeria na baya-bayan nan ya nuna yadda rayuwar masu fama da ciwon koda da dama a Kano ke dogara da injinan wankin kodar koda 12 kacal a manyan cibiyoyin kiwon lafiya guda biyu da suka hadar da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) da Asibitin kwararru na Abdullahi Wase.

A Asibitin kwararru na Abdullahi Wase a kalla majinyata dake da nasaba da koda, 160 ke ziyartar asibitin duk mako, haka akan sami sabbin masu kamuwa daga cutar mutum 15 dake zuwa duk makon.

Yayin da a Asibitin koyarwa na Aminu Kano akan sami majinyata kusan 70 a duk mako dake zuwa domin wankin kodar. Amma akalla ana ganin masu fama da cutar mutum 40, baya ga yadda da dama ke zaman jira.

Duk da tsadar wankin na koda, wasu daga cikin injinan wankin basa aiki yadda ya kamata.

Da yake jawabi a yayin mika kayayyakin aikin ga asibitin shugaban gidauniyar dashen kodar, Alhaji Ibrahim Abdullahi ya ce sun dauki wannan mataki ne domin rage radadi gami da wahalhalun da masu fama da lulurar ke fuskanta.

Ya kara da cewa sun dauki matakin tallafawa Asibitin na Abdullahi Wase ne sakamakon kokarin sa rage farashin kudin wankin koda ga masu fama da lalurar.

“Mun kashe sama da naira dubu dari biyar domin samar da kayan aikin wankin koda, don haka muna kira ga wasu kungiyoyi da masu hannun da shuni da suyi koyi da wannan abun Alkhari.

A nata jawabin, tsohuwar Ministar ilimi ta Nijeriya, Farfesa Rukayya Ahmad Rufa’I, wacce mamba ce a gidauniyar ta yi kira ga gwamnatin Jihar Kano da ta gaggauta daukar matakai domin magance kalubalen da asibitin ke fuskanta.

Babban Daraktan asibitin wanda ya sami wakilci Dr. Bashir Garba Ahmad ya yaba da irin hangen nesa da jajircewa da wannan gidauniya ta yi wajen rage radadin ga masu fama da lalurar.

Ya kara da cewa Asibitin na fuskantar kalubale masu tarin yawa, musamman na kayan da suka jibanci ayyukan lura da masu famada lalura koda, wanda ke bukatar gwamnatin jihar kano da masu ruwa da tsaki su gaggauta daukar mataki.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp