Home Labarai DHQ zata bada Miliyan Biyar ga wanda ke da bayani kan yadda...

DHQ zata bada Miliyan Biyar ga wanda ke da bayani kan yadda za’a cafke ‘yan ta’adda

Shalkwatan Tsaron Najeriya ya wallafa sunaye tare da hotunan wasu kwamandojin ‘yan ta’addar da suka addabi arewa maso gabashi da kuma arewa maso yammaci da tsakiyar arewacin Najeriya.

Shalkawatan tsaron ta ce, zata bada tukuicin Naira miliyan 5 ga duk wani dan Najeriya da ke da bayanai kan yadda za a iya cafke ‘yan ta’addar.

wannan dai na wani bangare na daukar matakin ci gaba da aikin kakkabe mayakan dake tayar da kayar baya a yankunan. abin da ta bayyana mayin aikin daya rataya a wuyan ta maido da da zaman lafiya a yankunan.

Sunayen ‘yan ta’addar da ake nema ruwa a jallo kamar yadda darektan yada labaran shalkwatan tsaron Manjo Janar Jimmy Akpor ya fitar, sun hadar da:

SANI DANGOTE – daga kauyen  Dumbarum, Karamar Hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.

BELLO TURJI GUDDA – daga kauyen Dakai, jihar Zamfara.

LEKO – daga kauyen Mozol, jihar Katsina.

DOGO NAHALI – daga kauyen ‘yar tsamiya, Karamar Hukumar  Kankara, jihar Katsina.

HALILU SUBUBU – daga kauyen Sububu a Karamar Hukumar Maradun, jihar Zamfara.

NAGONA –  daga Angwan Galadima da ke ISA a jihar S|okoto.

NASANDA – daga kauyen Kwashabawa, Karamar Hukumar Zurmi, jihar Zamfara.

ISIYA KWASHEN GARWA – daga kauyen Kamfanin Daudawa da ke Faskari a jihar Katsina.

ALI KACHALLA da aka fi sani da  ALI KAWAJE – daga kauyen Kuyambara a jihar Zamfara.

ABU RADDE – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

DAN-DA – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

SANI GURGU – daga kauyen Varanda a Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

UMARU DAN NIGERIA – daga kauyen Rafi da ke Mada a Gusau, jihar Zamfara.

NAGALA – daga Maru a jihar Zamfara.

ALHAJI ADO ALIERO – daga kauyen Yankuzo, a Karamar Hukumar Tsafe, jiharZamfara.

MONORE – daga ‘Yantumaki, jihar Katsina.

GWASKA DANKARAMI – daga kauyen Shamushele a Karamar Hukumar Zuri, jihar Zamfara.

BALERI – daga Karamr Hukumar Shinkafi, jihar Zamfara.

MAMUDU TAINANGE – daga kauyen baranda, Karamar Hukumar Batsari, jihar Katsina.

daga bisani shalkwatar ta ce ga dukkan mai wani karin bayani kan wadannan ‘yan ta’adda sai ya kira 09135904467 domin yin bayani.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp