Home General Dakarun Sojin Nijeriya Sun yi Barin wuta kan ‘yan Ta’adda a jihar...

Dakarun Sojin Nijeriya Sun yi Barin wuta kan ‘yan Ta’adda a jihar Kaduna

Rundunar sojin saman Najeriya ta kai wani samame ta sama a kan wasu gungun ƴan bindiga da aka gano a wasu wuraren da ke cikin wasu kananan hukumomin Kaduna, inda suka hallaka da dama da ga cikin su.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Kwamishinan tsaro da harkokin cikin , Samuel Aruwan, ya fitar aka raba ga manema labarai.

Ya ce an yi luguden wutar a kan ƴan ta’addan ne a yankin Kawara da ke karamar hukumar Igabi a wuraren da ‘yan bindigar samu maɓoya.

“An tabbatar da kashe ‘yan bindiga a harin na jirgin sama kuma wasu da aka yi garkuwa da su sun samu tserewa daga yankin gaba daya, kamar yadda wasu majiyoyi masu sahihanci na suka tabbatar.

 “Hakazalika, a Walawa, karamar hukumar Giwa, an kai hari a wani wuri da aka yi nasarar gano wa. A karamar hukumar Chikun, an gudanar da aikin sa ido a kan Faka, Kangon Kadi, Damba, Ungwan Turai, Galbi, Gwagwada da kewaye. An ga ‘yan ta’adda a nisan kilomita 4 daga Arewa maso Yamma da Godani, kuma duk an kashe su,” inji shi.  Aruwan ya ci gaba da cewa a Kuduru, an ga inda ‘yan ta’addan suka kai hari da rokoki.

Ya ce a karamar hukumar Igabi, an gudanar da ayyuka a kan Riyawa, Alhaji Isiaka, Rima, Riyawa, Rumana, Ungwan Liman, Mai Gishiri da kuma yankin filin jirgin sama na Kaduna ba tare da sojojin sun raunata ba.

Ya kuma kara da cewa an samu irin wannan lamarin a Sabon Birnin, Anaba, Malumi, Wusono da Kerawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp