Home DUNIYA WHO: Ebola ta Kashe Mutu 54 a kasar Uganda

WHO: Ebola ta Kashe Mutu 54 a kasar Uganda

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce cutar Ebola ta kashe mutane da yawansu ya kai 54 cikin kwanaki 55 da bullarta a Uganda, dai dai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar masu harbuwa da cutar.

Cikin rahoton da WHO ta fitar kan yadda cutar ta Ebola ke ci gaba da lakume rayuka a Uganda, ta ce yankin Mubende da ke tattara alkaluman na da mutane 29 cikin mutanen 54 da cutar ta kashe.

A cewar rahoton daga lokacin da cutar ta bulla a ranar 20 ga watan Satumba zuwa yanzu an samu mutane 137 da aka tabbatar sun kamu da ita yayinda wasu 65 kuma suka warke.

Hukumar ta WHO ta ce yankunan da cutar ta fi yaduwa a sassan Uganda sun kunshi Kassanda da Kyegegwa da kuma Kagadi baya ga Bunyangabu da Wakiso da kuma Masaka da Kampala.

WHO ta ce yankunan Mubende da Kassanda inda ta fi tsananta na jumullar mutum 63 da kuma 47 da zuwa yanzu ke jinyar cutar ta Ebola.

Dukkanin yankunan dai yanzu haka na karkashin killacewar kwanaki 21 a kokarin dakile yaduwar cutar, wanda ya sa tun daga ranar 10 ga watan nan ba a sake samun wanda ya harbu ba.

Cikin mutane dubu 2 da 187 da aka yi imanin sun yi mu’amala da masu dauke da cutar, sun kammala killacewar kwanaki 21 karkashin kulawar jami’an lafiya kuma mutum 1 da 908 basu harbu da cutar ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp