Home Labarai EFCC ta Cafke Mustapha Naira Mai Canjin Kudi a Abuja

EFCC ta Cafke Mustapha Naira Mai Canjin Kudi a Abuja

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ta EFCC ta cafke wani mutum mai suna Mustapha Muhammad, wanda aka fi sani da  Mustapha Naira bisa zargin yada jita-jita a fannin harkokin kudi a kasar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da hukumar ta ranar talata, wanda hukumar ta bayyana cewa ta kama shi ne ranar 12 ga watan nuwamba a yankin wuse zone B wadda ke matsayin cibiyar hada-hadar kasuwancin chanjin kudi a birnin tarayya Abuja.

Hukumar tace kame na guda cikin ayyukan da ta ke yin a tsaftace harkokin chanjin kudaden waje da kuma kawar da dukka masu kawo tasgaro a fannin da kuma yin zagon kasa ga tattalin arzikin kasar.

“wanda ake zargin yayi wasu bayanai masu amfani a daidai lokacin da ake tsaka da gudanar da bincike” a cewar EFCC.

Idan dai za’a iya tunawa hukumar EFCC ta kai sumame kasuwannin chanjin kudi, dake Nijeriya da suka hadar da jihohin legas, kano dama birnin tarayya kasar Abuja, wani bangare na dakatar da sauyin kudin kasar da Dalar Amurka abinda ake kallon ya kara sanya farashin dalar tashin gwauron zabi.

An zargi yadda wasu ke halasta kudin haram ta hanyar sauya su da dala, da nufin kada su yi asarar su sakamakon sake fasalin kudin kasar da Gwamnati tayi Shirin yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp