Home Labarai EFCC ta Cafke Mustapha Naira Mai Canjin Kudi a Abuja

EFCC ta Cafke Mustapha Naira Mai Canjin Kudi a Abuja

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ta EFCC ta cafke wani mutum mai suna Mustapha Muhammad, wanda aka fi sani da  Mustapha Naira bisa zargin yada jita-jita a fannin harkokin kudi a kasar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da hukumar ta ranar talata, wanda hukumar ta bayyana cewa ta kama shi ne ranar 12 ga watan nuwamba a yankin wuse zone B wadda ke matsayin cibiyar hada-hadar kasuwancin chanjin kudi a birnin tarayya Abuja.

Hukumar tace kame na guda cikin ayyukan da ta ke yin a tsaftace harkokin chanjin kudaden waje da kuma kawar da dukka masu kawo tasgaro a fannin da kuma yin zagon kasa ga tattalin arzikin kasar.

“wanda ake zargin yayi wasu bayanai masu amfani a daidai lokacin da ake tsaka da gudanar da bincike” a cewar EFCC.

Idan dai za’a iya tunawa hukumar EFCC ta kai sumame kasuwannin chanjin kudi, dake Nijeriya da suka hadar da jihohin legas, kano dama birnin tarayya kasar Abuja, wani bangare na dakatar da sauyin kudin kasar da Dalar Amurka abinda ake kallon ya kara sanya farashin dalar tashin gwauron zabi.

An zargi yadda wasu ke halasta kudin haram ta hanyar sauya su da dala, da nufin kada su yi asarar su sakamakon sake fasalin kudin kasar da Gwamnati tayi Shirin yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp