Home Labarai Ghana ta Gargadi ‘yan kasarta kan zuwa Nijeriya

Ghana ta Gargadi ‘yan kasarta kan zuwa Nijeriya

Gwamnatin Ghana ta gargadi ‘yan kasarta kan balaguro zuwa babban birnin tarayyar Najeriya Abuja saboda matsalar tsaro.

Wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ranar Laraba ta ce gargadin ya biyo bayan mawuyacin hali da ake ciki a babban birnin kasar da kuma umarnin da hukumomi Najeriya suka bayar na a rufe otal-otal da ke gidajen kwana.

Sanarwar ta ta bukaci ‘yan kasar Ghana da dole sai sun shiga birnin Abuja da su tabbaatar sun dauki matakin kariya da taka tsan-tsan, inda ma’aikatar za ta ci gaba da sanya ido kan yadda al’umara ke ganuna tare da bayar da bayanai ga jama’a idan lamarin ya daidaita.”

Ana yawan tafiye-tafiye tsakanin Ghana da Najeriya, manyan kasashe biyu mafi karfin tattalin arziki a yammacin Afirka.

Hakan na zuwa ne makonni bayan Amurka da wasu ofisoshin jakadancin kasashen waje sun yi gargadi game da tafiye-tafiye zuwa babban birnin Najeriya saboda barazanar ta’addanci.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta roki ‘yan kasar da su kwantar da hankulansu tana mai tabbatar musu da cewa jami’an tsaro na kokarin dakile duk wata barazanar ta’addanci.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp