Home DUNIYA AU na shirin kakabawa Chadi Takunkumi

AU na shirin kakabawa Chadi Takunkumi

Kwamitin zaman lafiya da tsaro na Tarayyar Afirka (PSC) ya fara wani muhimmin taro kan kasar Chadi domin nazari kan wani rahoton shugaban kungiyar kan rikice-rikicen baya-bayan nan da suka wakana baya ga duba yiwuwar kakabawa kasar takunkumi.

Mambobi 15 na wannan kwamiti da ke da alhakin kariya da warware rikice-rikicen kasashen Afirka za su yi nazari kan rahoton da shugaban gudanarwarta dan asalin kasar Chadi Moussa Faki Mahamat ya gabatar, rahotan da tuni ya yadu a kafofin sada zumunta tun gabanin gabatar da shi.

Rahotan mai shafuka takwas ya tabbatar da sahihancin sa, bashi da wani sauki ga mahuntan rikon kwaryar sojin Chadi karkashin jagorancin janar Mahamat Idriss Deby Itno.

Rahotan ya zargi gwamnatin rikon kwaryar Chadi da kin mutunta wa’adin watanni 18 na mika mulki ga fararen hula kamar yadda aka yi alkawari tun farko, kana sunyi biris da mutunta haramcin da aka sanya wa sojojin da ke kan mulki shiga takara a zabe mai zuwa, abin da shugaban hukumar ta AU Moussa Faki ke ganin biri ne yayi kama da mutun, don haka babu wani zabi face kakaba musu takunkumi.

Tuni wata majiya mai tushe ta tabbatar da fushin Ndjamena tun bayan yaduwar rahoton, inda suka ce kungiyar ci gaban tattalin arzikin kasashen Tsakiyar Afirka ke bibiyar lamuran ba hurumin AU ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp