Home DUNIYA AU na shirin kakabawa Chadi Takunkumi

AU na shirin kakabawa Chadi Takunkumi

Kwamitin zaman lafiya da tsaro na Tarayyar Afirka (PSC) ya fara wani muhimmin taro kan kasar Chadi domin nazari kan wani rahoton shugaban kungiyar kan rikice-rikicen baya-bayan nan da suka wakana baya ga duba yiwuwar kakabawa kasar takunkumi.

Mambobi 15 na wannan kwamiti da ke da alhakin kariya da warware rikice-rikicen kasashen Afirka za su yi nazari kan rahoton da shugaban gudanarwarta dan asalin kasar Chadi Moussa Faki Mahamat ya gabatar, rahotan da tuni ya yadu a kafofin sada zumunta tun gabanin gabatar da shi.

Rahotan mai shafuka takwas ya tabbatar da sahihancin sa, bashi da wani sauki ga mahuntan rikon kwaryar sojin Chadi karkashin jagorancin janar Mahamat Idriss Deby Itno.

Rahotan ya zargi gwamnatin rikon kwaryar Chadi da kin mutunta wa’adin watanni 18 na mika mulki ga fararen hula kamar yadda aka yi alkawari tun farko, kana sunyi biris da mutunta haramcin da aka sanya wa sojojin da ke kan mulki shiga takara a zabe mai zuwa, abin da shugaban hukumar ta AU Moussa Faki ke ganin biri ne yayi kama da mutun, don haka babu wani zabi face kakaba musu takunkumi.

Tuni wata majiya mai tushe ta tabbatar da fushin Ndjamena tun bayan yaduwar rahoton, inda suka ce kungiyar ci gaban tattalin arzikin kasashen Tsakiyar Afirka ke bibiyar lamuran ba hurumin AU ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp