Home DUNIYA AU na shirin kakabawa Chadi Takunkumi

AU na shirin kakabawa Chadi Takunkumi

Kwamitin zaman lafiya da tsaro na Tarayyar Afirka (PSC) ya fara wani muhimmin taro kan kasar Chadi domin nazari kan wani rahoton shugaban kungiyar kan rikice-rikicen baya-bayan nan da suka wakana baya ga duba yiwuwar kakabawa kasar takunkumi.

Mambobi 15 na wannan kwamiti da ke da alhakin kariya da warware rikice-rikicen kasashen Afirka za su yi nazari kan rahoton da shugaban gudanarwarta dan asalin kasar Chadi Moussa Faki Mahamat ya gabatar, rahotan da tuni ya yadu a kafofin sada zumunta tun gabanin gabatar da shi.

Rahotan mai shafuka takwas ya tabbatar da sahihancin sa, bashi da wani sauki ga mahuntan rikon kwaryar sojin Chadi karkashin jagorancin janar Mahamat Idriss Deby Itno.

Rahotan ya zargi gwamnatin rikon kwaryar Chadi da kin mutunta wa’adin watanni 18 na mika mulki ga fararen hula kamar yadda aka yi alkawari tun farko, kana sunyi biris da mutunta haramcin da aka sanya wa sojojin da ke kan mulki shiga takara a zabe mai zuwa, abin da shugaban hukumar ta AU Moussa Faki ke ganin biri ne yayi kama da mutun, don haka babu wani zabi face kakaba musu takunkumi.

Tuni wata majiya mai tushe ta tabbatar da fushin Ndjamena tun bayan yaduwar rahoton, inda suka ce kungiyar ci gaban tattalin arzikin kasashen Tsakiyar Afirka ke bibiyar lamuran ba hurumin AU ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp