Home General NNPC na neman kariyar sojoji domin fara hako man fetur a Borno

NNPC na neman kariyar sojoji domin fara hako man fetur a Borno

Kamfanin Man NNPC a Najeriya ya nemi taimakon rundunar soji ta 7 da ke da cibiya a Maiduguri da ta taimaka masa wajen bai wa ma’aikatan da za su yi aikin hako mai a gabar Tafkin Chadi kariyar da ake bukata.

Manjo Janar Ali Nani mai ritaya, ya jagoranci tawagar wasu mutane 3 domin ganawa da kwamandan runduna ta 7, Manjo Janar Waidi Shuaibu domin gabatar da bukatar da kuma tattaunawa kan yadda za a samu biyan bukata.

Sanarwar da kakakin rundunar ya gabatar, ta ce Janar Nani ya gabatar da bukatar ce a madadin kamfanin Didan wanda NNPC ya ba shi aikin hako man.

Kwamandan runduna ta 7 Janar Shuaibu ya yi alkawarin bai wa ma’aikatan tsaron da suke bukata domin gudanar da ayyukansu.

Janar Shuaibu ya ce rundunar za ta ci gaba da bada gudumawar da ta dace wajen kare lafiyar ma’aikatan da kuma kayan aikinsu, yayin da ake aikin sake gina yankin da rikicin Boko Haram ya shafa.

A shekarun baya, irin wannan yunkuri na kamfanin man ya gamu da koma baya lokacin da mayakan Boko Haram suka kama wasu daga cikin ma’aikatan da ke aiki a yankin.

Masana ma’adinai sun dade suna danganta Jihar Borno, musamman yankin Tafkin Chadi da arzikin man fetur da kuma iskar gas.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp