Home General CBN ya umarci dukkan bankunan kasuwanci na kasar da su fara biyan...

CBN ya umarci dukkan bankunan kasuwanci na kasar da su fara biyan masu ajiya a bankunan sababbin takardun naira

Babban bankin Najeriya CBN ya umarci dukkan bankunan kasuwanci na kasar da su fara biyan masu ajiya a bankunan sababbin takardun naira daga cikin bankunan ba kamar yadda ya umarce su da su rika biyansu ta na’urar cirar kudi ta ATM ba.

Wannan umarnin na zuwa ne bayan da harkokin kasuwanci suka kusan tsayawa cak bayan da gwamnatin Najeriya ta fitar da sababbin takrdun kudin na naira 200 da 500 da 1,000.

Cikin wata sanarwa da daraktan sadarwa na bankin Osita Nwanisobi ya sanya wa hannu, CBN ya lura da wasu miyagun halaye da ‘yan kasar ke nunawa na sayarwa da yin jifa da sababbin takardun kudin a iska da tattaka su yayin wasu bukukuwa.

Nwanisobi ya ce babban bankin ya hada gwiwa da rundunar ‘yan sandan Najeriya da hukumar tara haraji ta kasa da ta EFCC domin hukunta wadanda aka kama suna taka dokokin kasar, musamman wadanda suka jibanci yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa.

Bankin ya kuma gargadi ‘yan Najeriya da su guji halayyar wulakanta takardun kudin kasar musamman a yayin da suke bikin zagayowar ranar haihuwa da na aure da na binne mamata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp