Home General CBN ya umarci dukkan bankunan kasuwanci na kasar da su fara biyan...

CBN ya umarci dukkan bankunan kasuwanci na kasar da su fara biyan masu ajiya a bankunan sababbin takardun naira

Babban bankin Najeriya CBN ya umarci dukkan bankunan kasuwanci na kasar da su fara biyan masu ajiya a bankunan sababbin takardun naira daga cikin bankunan ba kamar yadda ya umarce su da su rika biyansu ta na’urar cirar kudi ta ATM ba.

Wannan umarnin na zuwa ne bayan da harkokin kasuwanci suka kusan tsayawa cak bayan da gwamnatin Najeriya ta fitar da sababbin takrdun kudin na naira 200 da 500 da 1,000.

Cikin wata sanarwa da daraktan sadarwa na bankin Osita Nwanisobi ya sanya wa hannu, CBN ya lura da wasu miyagun halaye da ‘yan kasar ke nunawa na sayarwa da yin jifa da sababbin takardun kudin a iska da tattaka su yayin wasu bukukuwa.

Nwanisobi ya ce babban bankin ya hada gwiwa da rundunar ‘yan sandan Najeriya da hukumar tara haraji ta kasa da ta EFCC domin hukunta wadanda aka kama suna taka dokokin kasar, musamman wadanda suka jibanci yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa.

Bankin ya kuma gargadi ‘yan Najeriya da su guji halayyar wulakanta takardun kudin kasar musamman a yayin da suke bikin zagayowar ranar haihuwa da na aure da na binne mamata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp