Home General El-Rufa’i ya Caccaki Wasu a Fadar Gwamnatin Tarayyar Nijeriya

El-Rufa’i ya Caccaki Wasu a Fadar Gwamnatin Tarayyar Nijeriya

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru El-Rufai yace akwai wasu “jami’ai” a fadar gwamnatin Najeriya ta Aso Rock a Abuja dake wa dan takarar shugaban kasar karkashin jam’iyyar APC mai mulkin Asiwaju Bola Tinubu, zagon kasa domin ya fadi zabe.

Da yake magana a wani shirin safe na gidan Talabijin na Channels, gwamnan ya ce wadannan mutanen da bai bayyana sunayensu ba suna cike da takaicin yadda Tinubu ya doke ‘yan takararsu a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC, abin da ya sa suka shiga shirya makarkashiya domin ya fadi zabe.

El-Rufai ya ce mutanen na fakewa ne da muradin shugaban kasa Muhammadu Buhari na yin abin da yake ganin ya dace.

“Suna kokarin ganin lallai sai mun fadi zabe, kuma suna fakewa da burin shugaban kasa na yin abin da yake ganin ya dace. Zan ba da misali guda biyu: wannan tallafin man fetur da ake kashewa tiriliyoyin Naira, tuni muka amince a janye”.

Malam Nasir El-Rufai yace yayi wata tattaunawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari a shekarar 2021, inda ya nuna masa illar dake cikin ware sama da Tiriliyan 2 wajen biyan tallafin man fetur alhali kuwa ana kashe Naira biliyan 200 kacal a kasafin kudin gudanar da manyan ayyuka.

Yace shugaban kansa ya gamsu, hakan kowa dake cikin gwamnati ya amince da batun cire tallafin.

Misali na biyu da Gwamna El-Rufai ya bayar shine batun sauya fasalin wasu takardun kudin Najeriya Naira. Yace ana daurawa gwamnan babban bankin Najeriya CBN wannan laifi, amma kuma ba haka bane.

“Jama’a na zargin Gwamnan Babban Bankin ne da laifin sake fasalin kudin, amma ba haka batun yake ba, ku tuna da mulkin Buhari na farko a soji; wato gwamnatin Buhari da Idiagbon sun canza mana kudin mu kuma sun yi haka a asirce da nufin kamo wadanda ke wawure kudaden haram”.

Yace hakan mataki ne mai kyau, kuma hakkin sa ne, to amma yin hakan a wannan lokaci bashi da ma’ana a fuskantar tattalin arziki da siyasa.

Kalaman El-Rufai na zuwa ne mako guda bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki Asiwaju Bola Tinubu yayi zargin ana shirya makarkashiya don hanashi samun nasara a zabe mai zuwa ciki harda tsadar mai da kuma batun canjin kudi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp