Home General El-Rufa’i ya Caccaki Wasu a Fadar Gwamnatin Tarayyar Nijeriya

El-Rufa’i ya Caccaki Wasu a Fadar Gwamnatin Tarayyar Nijeriya

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru El-Rufai yace akwai wasu “jami’ai” a fadar gwamnatin Najeriya ta Aso Rock a Abuja dake wa dan takarar shugaban kasar karkashin jam’iyyar APC mai mulkin Asiwaju Bola Tinubu, zagon kasa domin ya fadi zabe.

Da yake magana a wani shirin safe na gidan Talabijin na Channels, gwamnan ya ce wadannan mutanen da bai bayyana sunayensu ba suna cike da takaicin yadda Tinubu ya doke ‘yan takararsu a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC, abin da ya sa suka shiga shirya makarkashiya domin ya fadi zabe.

El-Rufai ya ce mutanen na fakewa ne da muradin shugaban kasa Muhammadu Buhari na yin abin da yake ganin ya dace.

“Suna kokarin ganin lallai sai mun fadi zabe, kuma suna fakewa da burin shugaban kasa na yin abin da yake ganin ya dace. Zan ba da misali guda biyu: wannan tallafin man fetur da ake kashewa tiriliyoyin Naira, tuni muka amince a janye”.

Malam Nasir El-Rufai yace yayi wata tattaunawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari a shekarar 2021, inda ya nuna masa illar dake cikin ware sama da Tiriliyan 2 wajen biyan tallafin man fetur alhali kuwa ana kashe Naira biliyan 200 kacal a kasafin kudin gudanar da manyan ayyuka.

Yace shugaban kansa ya gamsu, hakan kowa dake cikin gwamnati ya amince da batun cire tallafin.

Misali na biyu da Gwamna El-Rufai ya bayar shine batun sauya fasalin wasu takardun kudin Najeriya Naira. Yace ana daurawa gwamnan babban bankin Najeriya CBN wannan laifi, amma kuma ba haka bane.

“Jama’a na zargin Gwamnan Babban Bankin ne da laifin sake fasalin kudin, amma ba haka batun yake ba, ku tuna da mulkin Buhari na farko a soji; wato gwamnatin Buhari da Idiagbon sun canza mana kudin mu kuma sun yi haka a asirce da nufin kamo wadanda ke wawure kudaden haram”.

Yace hakan mataki ne mai kyau, kuma hakkin sa ne, to amma yin hakan a wannan lokaci bashi da ma’ana a fuskantar tattalin arziki da siyasa.

Kalaman El-Rufai na zuwa ne mako guda bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki Asiwaju Bola Tinubu yayi zargin ana shirya makarkashiya don hanashi samun nasara a zabe mai zuwa ciki harda tsadar mai da kuma batun canjin kudi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp