Home Labarai Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar DSS na...

Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar DSS na tsare Emefiele

Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar da hukumar DSS ta gabatar mata mai neman izinin ci gaba da tsare dakataccen babban bankin Najeriya, Godwin Emefile da kwanaki 14 a bisa ƙarin shaidun da tace ta tattara a kan shi.

Mai shari’a Hamza Muazu ya yi wasi da ƙarar, yana kafa hujja da saɓawa zaman kotu, tare da bayyana cewa kotun bata da hurumin sauraron buƙatar.

A ranar Talata, an samu jayayya tsakanin jami’an DSS da na hukumar kula da gidan gyaran hali ta Najeriya a kan wanda zai ci gaba da tsare Mr Emefiele bayan kotu ta bayar da belinsa.

DSS ta yi Allah-wadai da lamarin, kuma ta sha alwashin gudanar da bincike a kai.

Ita dai DSS tana zargin Emefiele da laifin mallakar bindiga da harsashi ba bisa ƙa’ida ba, zargin da kuma ya musanta.

Za a ci gaba da shari’arsa ne a ranar 14 ga watan Nuwamba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp