Home Labarai Bazoum ya magantu bayan Juyin Mulki a Nijar

Bazoum ya magantu bayan Juyin Mulki a Nijar

Shugaban kasar Nijar Mohamed Bazoum ya yi amfani da kafar sada zumunta ta yanar gizo a ranar alhamis din nan tare da shan alwashin kare dimokiradiyya kwana guda bayan hambarar da shi a wani juyin mulkin da sojoji suka yi.

Ministan harkokin wajen kasar Hassoumi Massoudou shi ma ya fitar da wani rubutu a dandalin X, wanda aka fi sani da Twitter, domin “dukkan masu ra’ayin dimokaradiyya da masu kishin kasa” su sa juyin mulkin ya gaza.

Bayanin nasu ya biyo bayan wani jawabi ne da sojoji suka yi daren ranar Laraba a gidan talabijin na kasar.

Inda suka sanar da cewa an cire Bazoum daga kan karagar mulki tare da dakatar da dukkan hukumomin jamhuriyar, wanda ke zama juyin mulki karo na bakwai a yammacin Afirka da tsakiyar Afirka tun shekara ta 2020.

A ranar Larabar da ta gabata ne jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka datse fadar shugaban kasar da ke Yamai babban birnin kasar tare da tare Bazoum a ciki.

Wannan ya haifar da damuwa a yanki da na duniya game da rashin zaman lafiya a kasar da ke zama babbar abokiyar kawance ga kasashen yammacin Turai da ke taimakawa wajen yaki da ta’addanci a yankin Sahel.

Har yanzu ana tsare da Bazoum a cikin fadar shugaban kasa da safiyar Alhamis din nan, Massoudou ya fada a wata hira da kafar yada labaran Faransa ta France 24. Ba a san inda ministan yake ba.

Yamai shiru da sanyin safiyar Alhamis din nan yayin da ‘yan kasar suka farka da rufe kan iyakokin kasar da dokar hana fita da sojoji suka kafa a fadin kasar

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp