Home Labarai Bazoum ya magantu bayan Juyin Mulki a Nijar

Bazoum ya magantu bayan Juyin Mulki a Nijar

Shugaban kasar Nijar Mohamed Bazoum ya yi amfani da kafar sada zumunta ta yanar gizo a ranar alhamis din nan tare da shan alwashin kare dimokiradiyya kwana guda bayan hambarar da shi a wani juyin mulkin da sojoji suka yi.

Ministan harkokin wajen kasar Hassoumi Massoudou shi ma ya fitar da wani rubutu a dandalin X, wanda aka fi sani da Twitter, domin “dukkan masu ra’ayin dimokaradiyya da masu kishin kasa” su sa juyin mulkin ya gaza.

Bayanin nasu ya biyo bayan wani jawabi ne da sojoji suka yi daren ranar Laraba a gidan talabijin na kasar.

Inda suka sanar da cewa an cire Bazoum daga kan karagar mulki tare da dakatar da dukkan hukumomin jamhuriyar, wanda ke zama juyin mulki karo na bakwai a yammacin Afirka da tsakiyar Afirka tun shekara ta 2020.

A ranar Larabar da ta gabata ne jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka datse fadar shugaban kasar da ke Yamai babban birnin kasar tare da tare Bazoum a ciki.

Wannan ya haifar da damuwa a yanki da na duniya game da rashin zaman lafiya a kasar da ke zama babbar abokiyar kawance ga kasashen yammacin Turai da ke taimakawa wajen yaki da ta’addanci a yankin Sahel.

Har yanzu ana tsare da Bazoum a cikin fadar shugaban kasa da safiyar Alhamis din nan, Massoudou ya fada a wata hira da kafar yada labaran Faransa ta France 24. Ba a san inda ministan yake ba.

Yamai shiru da sanyin safiyar Alhamis din nan yayin da ‘yan kasar suka farka da rufe kan iyakokin kasar da dokar hana fita da sojoji suka kafa a fadin kasar

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp