Home Labarai Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar DSS na...

Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar DSS na tsare Emefiele

Wata babbar kotu a Abuja ta yi watsi da buƙatar da hukumar DSS ta gabatar mata mai neman izinin ci gaba da tsare dakataccen babban bankin Najeriya, Godwin Emefile da kwanaki 14 a bisa ƙarin shaidun da tace ta tattara a kan shi.

Mai shari’a Hamza Muazu ya yi wasi da ƙarar, yana kafa hujja da saɓawa zaman kotu, tare da bayyana cewa kotun bata da hurumin sauraron buƙatar.

A ranar Talata, an samu jayayya tsakanin jami’an DSS da na hukumar kula da gidan gyaran hali ta Najeriya a kan wanda zai ci gaba da tsare Mr Emefiele bayan kotu ta bayar da belinsa.

DSS ta yi Allah-wadai da lamarin, kuma ta sha alwashin gudanar da bincike a kai.

Ita dai DSS tana zargin Emefiele da laifin mallakar bindiga da harsashi ba bisa ƙa’ida ba, zargin da kuma ya musanta.

Za a ci gaba da shari’arsa ne a ranar 14 ga watan Nuwamba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp