Gwamnatin Rasha ta nesanta kanta da wasu masu zanga-zanga a Najeriya waɗanda aka gani suna ɗaga tutar ƙasar Rasha.
A ranar Litinin an ga tuɗaɗowar ɗumbin masu zanga -zanga a jihohin arewacin Najeriya kamar Zamfara da Kaduna, inda wasu daga cikinsu ke ɗaga tutar Rasha.
Sai dai a wata sanarwa da aka sanya a shafin na intanet, ofishin jakadancin Rasha a Najeriya ya ce matakin da wasu masu zanga-zanga suka ɗauka na amfani da tutar Rasha mataki ne na ƙashin kansu, kuma wannan ba shi ne ainahin manufa da muradin ƙasar Rasha ba.
Sanarwar ta ce: “Kamar a kodayaushe, muna sake jaddada cewa Rasha ba ta shiga cikin harkokin cikin gida na ƙasashe masu ƴanci, ciki kuwa har da Najeriya.”
Read Also:
Rasha ta ce tana martaba mulkin dimokuraɗiyyar Najeriya kuma tana kyautata zaton cewa zanga-zangar da ake yi a ƙasar na kan doka da kuma tsari na mulkin demokuraɗiyya.
Sanarwar ta kammala da cewa “sai dai za mu yi Allah-wadai idan wannan zanga-zanga ta rikiɗe zuwa tarzoma.”
Dubban masu zanga-zanga ne suka hau kan titunan biranen Najeriya a zanga-zangar adawa da matsin rayuwa da al’ummar ƙasar ke ciki.
Zanga-zangar ta ci gaba a ranar Litinin bayan da ƙungiyoyin da ke jagorantarta suka ce jawabin da shugaban ƙasar ya yi a ranar Lahadi bai taɓo buƙatunsu ba.
An tsara gudanar da zanga-zangar ne tsawon kwana goma, daga 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024.
PRNigeria Hausa












