Home Labarai Rasha ta Magantu kan Zanga-zangar Nijeriya

Rasha ta Magantu kan Zanga-zangar Nijeriya

Gwamnatin Rasha ta nesanta kanta da wasu masu zanga-zanga a Najeriya waɗanda aka gani suna ɗaga tutar ƙasar Rasha.

A ranar Litinin an ga tuɗaɗowar ɗumbin masu zanga -zanga a jihohin arewacin Najeriya kamar Zamfara da Kaduna, inda wasu daga cikinsu ke ɗaga tutar Rasha.

Sai dai a wata sanarwa da aka sanya a shafin na intanet, ofishin jakadancin Rasha a Najeriya ya ce matakin da wasu masu zanga-zanga suka ɗauka na amfani da tutar Rasha mataki ne na ƙashin kansu, kuma wannan ba shi ne ainahin manufa da muradin ƙasar Rasha ba.

Sanarwar ta ce: “Kamar a kodayaushe, muna sake jaddada cewa Rasha ba ta shiga cikin harkokin cikin gida na ƙasashe masu ƴanci, ciki kuwa har da Najeriya.”

Rasha ta ce tana martaba mulkin dimokuraɗiyyar Najeriya kuma tana kyautata zaton cewa zanga-zangar da ake yi a ƙasar na kan doka da kuma tsari na mulkin demokuraɗiyya.

Sanarwar ta kammala da cewa “sai dai za mu yi Allah-wadai idan wannan zanga-zanga ta rikiɗe zuwa tarzoma.”

Dubban masu zanga-zanga ne suka hau kan titunan biranen Najeriya a zanga-zangar adawa da matsin rayuwa da al’ummar ƙasar ke ciki.

Zanga-zangar ta ci gaba a ranar Litinin bayan da ƙungiyoyin da ke jagorantarta suka ce jawabin da shugaban ƙasar ya yi a ranar Lahadi bai taɓo buƙatunsu ba.

An tsara gudanar da zanga-zangar ne tsawon kwana goma, daga 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp