Home Labarai An kama telan dake dinka Tutar Rasha ga masu Zanga-Zanga a Kano

An kama telan dake dinka Tutar Rasha ga masu Zanga-Zanga a Kano

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya, ta sanar da kama wani Ahmed Tela, wanda take zargi da dinka tutocin kasar Rasha da wasu masu zanga-zanga ke amfani da su a lokacin zanga-zanga a Kano da wasu jihohin Arewa.

An kuma kama masu zanga-zanga kimanin 30 da ke dauke da tutocin tare da tsare su.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a hedikwatar hukumar ta farin kaya (DSS) a wani taron manema labarai da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro ya shirya.

An hangi yadda wasu masu zanga-zangar ke fitowa kan manyan titunan Nijeriya musamman jihohin Kano, Kaduna, Bauchi da wasu jihohin Arewacin Nijeriya dauke da tutocin kasar Rasha musamman a wannan rana ta 5 da fara Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a kasar.

An ga masu zanga-zangar dauke da tutocin kasar Rasha suna zagaya tituna suna rera wakoki daban-daban tare da wasu dauke da alluna.

Adejobi ya ce daga tutocin wasu kasashe a Najeriya, wadda aka kasa ce mai cin gashin kanta, laifi ne, inda ya kara da cewa wadanda aka kama da wadanda suka dauki nauyinsu za a tuhume su kamar yadda dokar kasar ta tanada kan laifukan da suka aikata.

“Da safiyar yau ne muka kama wani ‘Ahmed Tela’ daga karamar hukumar Nasarawa a jihar Kano, bisa laifin samar da tutocin kasar Rasha masu yawan gaske da ake baiwa matasan Najeriya domin su dagawa.

“Mun kama shi, Kuma muna kara farautar wasu musamman wadanda suka sa ka su. Kamar yadda nake magana da ku, haka abin ya faru a Kaduna. mun sami damar kama 30 daga cikinsu dauke da tutocin Rasha ” in ji babban jami’in ‘yan sandan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp