Home Labarai Abin da PDP ke cewa kan jawabin Shugaban kasa Tinubu

Abin da PDP ke cewa kan jawabin Shugaban kasa Tinubu

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya (PDP) ta ce jawabin da shugaban ƙasar Bola Tinubu ya gabatar a ranar Lahadi, game da zanga-zangar da ke gudana a faɗin ƙasar bai taɓo abubuwan da masu zanga-zangar ke kokawa a kai ba.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi, wadda ta samu sa hannun sakataren yaɗa labarun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba, PDP ta ce “jawabin na Tinubu ya nuna yadda ƙarara, Jama’iyyar APC da shugaba Tinubu ba su damu da halin ƙunci da al’ummar ƙasar ke fama da shi ba.”

Tinubu dai ya yi jawabin ne kwana huɗu bayan da wasu matasa a Najeriya suka hau kan tituna domin nuna fushi kan halin matsin tattalin arziƙi da al’ummar ƙasar ke fama da shi.

A cikin jawabin da ya gabatar da safiyar Lahadi, Tinubu ya buƙaci al’ummar ƙasar su yi haƙuri su dakatar da zanga-zangar ganin cewa ta yi sanadiyyar rasa rayuka a wasu jihohin ƙasar.

Zanga-zangar wadda ta fara a ranar Alhamis ta rikiɗe zuwa rikici a wasu jihohin ƙasar, lamarin da ya kai ga asarar rayuka da dukiyar al’umma.

Sanarwar da PDP ta fitar ta ci gaba da cewa “Jam’iyyar ta yi takaicin yadda ya kasa bayyana ƙwararan matakan da ya kamata a ce gwamnati ta ɗauka domin kawo wa al’umma sauƙin matsin da suke ciki a ƙasar.

“Shugaban ƙasa ya kasa yin bayani kan buƙatun al’umma na ɗaukara matakan da za su rage tsadar man fetur da magance faɗuwar darajar naira da kuma samar da abinci ga al’ummar da ke cikin yunwa,” in ji sanarwar.

Shi dai Tinubu a jawabin nasa na ranar Lahadi, ya ce gwamnatinsa ta ɗauki matakai kamar na shirin bai wa ɗalibai bashin karatu, da raba wa jihohi maƙudan kuɗaɗe da kuma bayar da tallafin abinci ta hannun gwamnoni.

Sai dai masharhanta da dama sun soki jawabin na Tinubu, inda suka ce ya gaza taɓo buƙatun masu zanga-zangar kai-tsaye.

Kuma tuni ƙungiyoyin da suke jagorantar zanga-zangar suka lashi takobin ci gaba da gudanar da ita a yau Litinin.

Ƙungiyoyin kare hakkin bil’adama dai sun zargi jami’an gwamnati da bude wuta kan masu zanga-zanga, kuma sun buƙaci hukumomi su yi bincike a kai.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp