Home Labarai An saka dokar hana fita a jihar Kaduna

An saka dokar hana fita a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a babban birnin jihar da kuma Zariya.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne “bayan nazarin yanayin tsaro a jihar sakamakon tarzomar da aka samu” biyo bayan zanga-zangar da ake yi a sassan Najeriya saboda kuncin rayuwa.

Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar ta hannun kwamishina mai lura da harkokin tsaro a jihar, Samuel Aruwan ta ce “akwai ƙwararan hujjoji da ke nuna cewa ɓata gari sun ƙwace zanga-zangar, waɗanda suka koma satar kaya da ɓarnata dukiyar gwamnati.”

Gwamnatin ta shawarci al’ummar jihar da su kiyaye da doka da kuma kasancewa a cikin gida, a yayin da jami’an tsaro kuma za su ci gaba da aiki don tabbatar da tsaron lafiyar al’umma.

Jihar kaduna, ta zamo ta baya-bayannan da aka sanya dokar hana fita saboda yadda zanga-zangar ta rikiɗe zuwa tarzoma.

Kaduna na daga cikin jihohin da aka sanar cewa an samu asarar rayuka tun bayan ɓarkewar zanga-zangar a ranar Alhamis.

An sanya irin wannan dokar a jihohin Kano da Jigawa da Borno da Yobe da Katsina da kuma Filato.

Kodayake, an dage dokar a wasu jihohin, yayin da a wasu kuma aka sassauta dokar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp