Home Labarai An saka dokar hana fita a jihar Kaduna

An saka dokar hana fita a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a babban birnin jihar da kuma Zariya.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne “bayan nazarin yanayin tsaro a jihar sakamakon tarzomar da aka samu” biyo bayan zanga-zangar da ake yi a sassan Najeriya saboda kuncin rayuwa.

Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar ta hannun kwamishina mai lura da harkokin tsaro a jihar, Samuel Aruwan ta ce “akwai ƙwararan hujjoji da ke nuna cewa ɓata gari sun ƙwace zanga-zangar, waɗanda suka koma satar kaya da ɓarnata dukiyar gwamnati.”

Gwamnatin ta shawarci al’ummar jihar da su kiyaye da doka da kuma kasancewa a cikin gida, a yayin da jami’an tsaro kuma za su ci gaba da aiki don tabbatar da tsaron lafiyar al’umma.

Jihar kaduna, ta zamo ta baya-bayannan da aka sanya dokar hana fita saboda yadda zanga-zangar ta rikiɗe zuwa tarzoma.

Kaduna na daga cikin jihohin da aka sanar cewa an samu asarar rayuka tun bayan ɓarkewar zanga-zangar a ranar Alhamis.

An sanya irin wannan dokar a jihohin Kano da Jigawa da Borno da Yobe da Katsina da kuma Filato.

Kodayake, an dage dokar a wasu jihohin, yayin da a wasu kuma aka sassauta dokar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp