Home Labarai WAI ta zargi ‘yan sanda da amfani da karfin daya wuce kima...

WAI ta zargi ‘yan sanda da amfani da karfin daya wuce kima akan masu Zanga-Zanga

Kungiyar War Against Injustice tayi Allah wadai da  kasha mutane a wasu unguwannin jihar Kano, yawan wata arangama da dakarun tsaro a lokacin zanga-zanagr tsadar rayuwa a jihar.

Shugaban kungiyar Kwamared Umar Ibrahim Umar, ne ya bayyana hakan inda yace an hallaka mutane  unguwannin na Kurna, Rijiyar Lemo, da Sharaɗa a jihar, da wasu sassan Najeriya.

Muna kira ga rundunar ‘yan sandan Najeriya da sauran masu ruwa da tsaki da su gaggauta binciki wadannan zarge-zarge tare da daukar matakin da ya dace kan masu aikata laifin.

Haka kuma muna kira ga masu ruwa da tsaki da su ba mu hadin kai wajen neman adalci ga wadanda abin ya shafa da iyalansu. Muna neman a ba da cikakken bayani kan rayukan da aka rasa da kuma jikkatar da aka samu a lokacin zanga-zangar.

Yin amfani da karfi kan masu zanga-zangar lumana cin zarafi ne da take hakkin bil’adama da ‘yancin walwala. Za mu ci gaba da bayar da shawarwarin kare wadannan hakkoki tare da neman a gurfanar da wadanda ke da hannu a wannan ta’asa.

Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda abin ya shafa tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp