Home Labarai Majalisar Dattijai ta yi wa Obasanjo Martani

Majalisar Dattijai ta yi wa Obasanjo Martani

Majalisar dokokin Nijeriya ta mayar wa tsohon shugaban kasar Cif Olusegun Obasanjo martani game da kalamansa kan kudaden albashin ƴan majalisar.

A ranar Juma’a ne dai tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo wanda ya sha sukar gwamnati ya yi zargi ƴan majalisar cewa su ke yanka kansu albashi mai tsoka da kuma hanyoyin da suke samu kuɗi fiye da ƙima.

A cewar tsohon shugaban, hukumar tattara kudaden shiga da raba su ta Najeriya ce ya kamata ta yanke hukunci kan albashin da kowane ma’aikaci zai karɓa.

A martaninta, majalisar dokokin ta ce duk abun da ake ba wa ƴan majalisar na kan tsari tare da cewa ba su ke yankawa kansu albashi ba.

sai dai ta cikin wata sanarwa da kakakin majalisar dattawa Yemi Adaramodu ya fitar ranar Lahadi, ya bayyana ikirarin tsohon shugaban a matsayin “marar tushe”.

Wannan cacar baki na zuwa a daidai lokacin da ake fama da tsadar rayuwa a Najeriya.

A shekarun baya baya nan ɓangaren majalisar dokokin Najeriya na daga ɓangaren gwamnati da galibin mutane musaman ma masu sharhi kan al’amurran yau da kullum da ƙungiyoyin fararen hula ke zargin cewa abubuwan da suke samu na wuce ka’idar da ya kamata a ce ana ba su a matsayin haƙƙoƙinsu na yi wa alumma dokoki.

Wasu ƙungiyoyi da ƴan Najeriya sun ta nuna tsaya ga ƴan majalisar a kan zargin yadda suke laftawa kansu kudin mazaɓu a kasafin kuɗi wanda wasu ke ganin sun fifita kansu.

A wasu lokutan ma wasu ƴan majalisar da kansu sun fito sun koka kan cewa ana nuna bambanci a rabon kuɗin mazabun.

A yanzu kuma tsohon shugaban kasar Nijeriya Cif Olusegun Obasanjo ne ya soki ‘yan majalisar kan cewar suna yankawa kansu albashi da kuma samun kuɗi masu gwaɓi daga fadar shugaban kasa.

‘’Kudin jarida, alawus din ɗan kamfai da kudin bahaya, kuma kuna ba kanku abubuwa barkatai, cikin girmamawa kun san hakan ba daidai ba ne a ce ina yankawa kaina albashi, majalisar dattawa na yin haka, har ma tinkaho kuke yi da haka’’ in ji Obasanjo.

Tsohon shugaban kasar ya kuma yi zargin cewa ana bai wa dukannin ‘yan majalisar naira miliyan 200.

Awwal Musa Rafsanjani na kungiyar CISLAC mai sa ido kan harkokin Majalisun dokokin kasar ya ce akwai ƙamshin gaskiya a kalaman tsohon shugaban kasar:

‘’Akwai wasu kudade da a duk lokacin da za su tafi aikace-aikace ba ya cikin alawus -alawus dinsu, baya cikin albashinsu , hatta taron jin bahasin jama’a suna karbar alawus- alawus’’ in ji shi

Rafsanjaji ya yi gargadin idan har ba a kawo karshen wannan matsalar ba, to ba za a daina rigimar siyasa da rigimar zabe ba.

A cewarsa “idan mutane sun san cewa idan suka zo majalisa za su sami irin wadannan makuɗan kudade na Halak da na haram to za a ci gaba da samun rikici lokacin zabe”

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp