Home Bincike BINCIKE: Shin da Gaske ne Limamai da Fastoci, sun jagoranci zanga-zangar ‘Endbadgovernance’...

BINCIKE: Shin da Gaske ne Limamai da Fastoci, sun jagoranci zanga-zangar ‘Endbadgovernance’ A Garin Jos?

Wani bidiyo da aka yaɗa a manhajar WhatsApp, ya yi ikirarin cewa wasu limamai da malaman majami’u a jihar Filato sun ja ragamar gudanar da zanga-zangar kin jinin gwamnatin Bola Ahmad Tinubu.

Mafi akasarin mutanen na tafiya ne sanye da baƙaƙen kaya, dauke da alamun addinin kirista da alamar gicciye (cross) a wuyan su, a gefe kuma ga wani mutum sanye da kayan hausawa. Sun riƙe hannu yayin da suke gudanar da zanga-zangar.

PRNigeria ta raba bidiyon gida-gida inda ta gudanar da binciken sahihancin hoto ta hanyar yin amfani da salon (reverse image search).

Sakamakon ya nuna cewa bidiyon ya fito ne daga jihar ta Filato a lokacin da ake gudanar da tattakin zaman lafiya, bisa jagorancin shugaban ƙungiyar CAN Rev. Polycarp Lubo, sai kuma shugaban majami’ar ECWA Rev. Dr. Stephen Panya, ya shiga ciki da sauran shuwagabannin kungiyoyin kirista a watan Janairun 2024. Wanda tattakin na su na nuna rashin gamsuwa da kisan mutane sama da 200 da aka yi a ranar bikin kirsimeti a kananan hukumomin Bokkos da Barkin Ladi dake jihar.

Tattakin da ya sami halartar mabiya addinin kirista da dama da hadin gwiwar mazauna yanki, wanda suka taro a gidan Gwamnatin jihar da ke garin Jos, ya yin da gwamnan jihar Caleb Mutfwang ya tarbe su.

Shuwagabannin kiristocin sun buƙaci gwamnatin jihar ta dauki matakin da ya dace na kare rayuka da dukiyoyin al’umma ga wadanda ke hallakasu ba ji ba gani.

Wani bincike ya nuna cewa mutane da dama sun wallafa bidiyon a shafukan su na X wanda aka fi sani da twitter, tare da laƙabin “tattakin zaman lafiya daga shuwagabannin kirista” #StopTheKillings.

PRNigeria ta jiyo wakokin ibada na addinin kirista cikin harshen hausa, suna kuma kaɗa korayen ganye da ke hannayen su.

KAMMALAWA: bisa ga hujjojin da PRNigeria ta tattara sun tabbatar da cewa Limamai da Malaman Majami’u basu jagoranci wani gangami ko tattaki na ‘EndBadGovernance’ a garin Jos da ke jihar Filato ba.

Amma, abin da ma su iƙirarin suka gani matsayin zanga-zanga, to tattaki ne na zaman lafiya na daruruwan al’umma mabiya addinin kirista a kananan hukumomin Bokkos da Barkin Ladi suka gudanar.

Don haka, PRNigeria ta tabbatar da ikirarin da aka yi na cewa malaman Addini sun haɗa gwiwa don kalubalantar yadda Tinubu ke gudanar da Gwamnatinsa Karya ce a bayyana ne.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp