Home Bincike BINCIKE: Shin da Gaske ne Limamai da Fastoci, sun jagoranci zanga-zangar ‘Endbadgovernance’...

BINCIKE: Shin da Gaske ne Limamai da Fastoci, sun jagoranci zanga-zangar ‘Endbadgovernance’ A Garin Jos?

Wani bidiyo da aka yaɗa a manhajar WhatsApp, ya yi ikirarin cewa wasu limamai da malaman majami’u a jihar Filato sun ja ragamar gudanar da zanga-zangar kin jinin gwamnatin Bola Ahmad Tinubu.

Mafi akasarin mutanen na tafiya ne sanye da baƙaƙen kaya, dauke da alamun addinin kirista da alamar gicciye (cross) a wuyan su, a gefe kuma ga wani mutum sanye da kayan hausawa. Sun riƙe hannu yayin da suke gudanar da zanga-zangar.

PRNigeria ta raba bidiyon gida-gida inda ta gudanar da binciken sahihancin hoto ta hanyar yin amfani da salon (reverse image search).

Sakamakon ya nuna cewa bidiyon ya fito ne daga jihar ta Filato a lokacin da ake gudanar da tattakin zaman lafiya, bisa jagorancin shugaban ƙungiyar CAN Rev. Polycarp Lubo, sai kuma shugaban majami’ar ECWA Rev. Dr. Stephen Panya, ya shiga ciki da sauran shuwagabannin kungiyoyin kirista a watan Janairun 2024. Wanda tattakin na su na nuna rashin gamsuwa da kisan mutane sama da 200 da aka yi a ranar bikin kirsimeti a kananan hukumomin Bokkos da Barkin Ladi dake jihar.

Tattakin da ya sami halartar mabiya addinin kirista da dama da hadin gwiwar mazauna yanki, wanda suka taro a gidan Gwamnatin jihar da ke garin Jos, ya yin da gwamnan jihar Caleb Mutfwang ya tarbe su.

Shuwagabannin kiristocin sun buƙaci gwamnatin jihar ta dauki matakin da ya dace na kare rayuka da dukiyoyin al’umma ga wadanda ke hallakasu ba ji ba gani.

Wani bincike ya nuna cewa mutane da dama sun wallafa bidiyon a shafukan su na X wanda aka fi sani da twitter, tare da laƙabin “tattakin zaman lafiya daga shuwagabannin kirista” #StopTheKillings.

PRNigeria ta jiyo wakokin ibada na addinin kirista cikin harshen hausa, suna kuma kaɗa korayen ganye da ke hannayen su.

KAMMALAWA: bisa ga hujjojin da PRNigeria ta tattara sun tabbatar da cewa Limamai da Malaman Majami’u basu jagoranci wani gangami ko tattaki na ‘EndBadGovernance’ a garin Jos da ke jihar Filato ba.

Amma, abin da ma su iƙirarin suka gani matsayin zanga-zanga, to tattaki ne na zaman lafiya na daruruwan al’umma mabiya addinin kirista a kananan hukumomin Bokkos da Barkin Ladi suka gudanar.

Don haka, PRNigeria ta tabbatar da ikirarin da aka yi na cewa malaman Addini sun haɗa gwiwa don kalubalantar yadda Tinubu ke gudanar da Gwamnatinsa Karya ce a bayyana ne.

By PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp