Home DUNIYA Kwamitin yakin neman zaben Trump ya zargi Iran

Kwamitin yakin neman zaben Trump ya zargi Iran

Kwamitin yaƙin neman zaɓen tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce an yi masa kutse a cikin bayanansa na cikin gida, kuma ya nuna alamun jami’an Iran ne ke yin hakan.

Shafin jaridar intanet ta Politico da ke Amurka, a jiya Asabar ya bayar da rahoton cewa an aika masa wasu takardun yaƙin neman zaɓe ciki har da takardun bincike na cikin gida da kwamitin yaƙin neman zaɓen na Trump ya yi a kan mataimakin Trump ɗin a zaɓen da za a yi, Sanatan Ohio, JD Vance.

Wani mai magana da yawun kwamitin yaƙin neman zaɓen ya gaya wa BBC cewa :“An samu waɗannan takardu ne ta haramtacciyar hanya daga wasu kafofi na ƙasar waje, da ke gaba da Amurka, da nufin katsa-landan a zaɓen 2024.”

Jaridar Politico ta ce ta tabbatar da sahihancin takardun, ko da yake wasu jaridu na duniya basu tabbatar da sahihancin ba.

Sai dai kwamitin yaƙin neman zaɓen bai bayar da cikakken bayani ko wata sheda da ke tabbatar da takardun da aka yi satar fitar da su ba ga masu kutse na Iran ko kuma gwamnatin Iran.

Ko a lokacin zaɓen shugaban Amurka na 2020 kamfanin Microsoft ya fitar da irin wannan rahoton, da cewa masu kutse na Iran na harin yaƙin neman zaɓe na shugaban ƙasa.

Kamfanin ya ma ƙara da cewa masu kutsen na Iran sun yi haka a kai-a kai aƙalla a zaɓe uku na shugaban ƙasa a Amurka.

Haka su ma jami’an tsaron Amurka sun yi gargaɗin cewa Iran na shirin hallaka Donald Trump, to amma wannan ba shi da alaka da harin da aka kai masa a watan da ya wuce a Pennsylvania.

Kuma a ranar Talata ma’aikatar shari’a ta Amurka ta tuhumi wani ɗan Pakistan da ake zargi yana da alaƙa da Iran da shirin kashe jami’an Amurka, wanda a iya cewa har ma da shugaban ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp