Home Labarai SERAP ta bukaci Tinubu ya binciki bashin dala biliyan 1.5 da jihohi...

SERAP ta bukaci Tinubu ya binciki bashin dala biliyan 1.5 da jihohi 36 suka karbo

Kungiyar  dake yaki da cin hanci da daidaito na harkokin gwamnati SERAP ta bukaci shugaban kasa Bola Tinubu ya binciki bashin dala biliyan 1.5 na bankin duniya da jihohi 36 suka karbo tare da babban birnin tarayya.

Kungiyar ta kuma bukaci Tinubu da ya binciki zargin karkatar da lamunin China na $3.121bn da gwamnatin tarayya ta tarba.

SERAP ta roki Shugaban kasa da ya umarci Babban antoni janar na kasa kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, da hukumomin da suka dace da yaki da cin hanci da rashawa da su gaggauta yin bincike sosai kan yadda aka kashe rancen, ta yadda za a rage “talauci da inganta rayuwar al’umma a fadin jihohin kasarnan.”

Hakan na kunshe ne a wata budaddiyar wasika mai kwanan watan Agusta 10, 2024, mai dauke da sa hannun Mataimakin Daraktan kungiyar, Kolawole Oluwadare.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp