Home Bincike Rikici tsakanin Boko Haram da ISWAP ya yi ajalin mayaƙa sama da

Rikici tsakanin Boko Haram da ISWAP ya yi ajalin mayaƙa sama da

Rahotanni daga yankin arewa maso gabashin Najeriya na nuna cewa rikicin cikin gida tsakanin ɓangaren Boko Haram da tsagin ISWAP ya yi sanadiyar mutuwar aƙalla mayaƙa guda 200 a tsakaninsu.

Kafar AFP ta ruwaito cewa ricikin ya yi ƙamari ne a tsakanin ɓangarorin ƙungiyar guda biyu a yankin Dogon Chiku da ke gaɓar Tekun Chadi a ranar Lahadi, wanda ya kasance ɗaya daga rigingimu da ya fi zafi saboda bambancin ra’ayi.

“Mun ƙirga aƙalla gawarwaki guda 200,” in ji wani mai suna Babakura Kolo a zantawarsa a AFP.

Wani tubabben ɗan Boko Haram da ke bibiyar harkokinsu da ya ce a kira shi da suna Saddiku ma ya tabbatar da rikicin, inda ya ce, “an kashe aƙalla ƴan ISWAP 200 a rigimar, sannan an kwashe muku makamai da dama, sannan aka kashe ƴan tsagin Boko Haram guda huɗu.”

Ya ƙara da cewa wannan ne rigima mafi zafi da aka yi a tsakanin ɓangarorin mayaƙan guda biyu tun bayan rabewarsu saboda saɓanin fahimta a shekarar 2016.

Wata majiyar tsaro ma ta tabbatar da aukuwar rigimar, inda ta ce “muna da bayanan sirri kan rigimar, kuma mun samu labarin mutuwar mayaƙa sama da 150, wanda kuma labari ne mai kyau a wajenmu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp