Home Labarai Likitoci masu neman ƙwarewa na yajin aiki a Najeriya

Likitoci masu neman ƙwarewa na yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa Najeriya (NARD) sun fara yajin aiki na dindindin daga ranar Asabar, lamarin da ya tsayar da ayyuka da dama a cibiyoyin kiwon lafiya a faɗin ƙasar.

Shugaban NARD, Dakta Mohammad Suleiman, ya tabbatar da fara yajin aikin a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar.

Wannan yajin aiki na zuwa ne bayan cikar wa’adin kwanaki 30 da ƙungiyar ta bai wa gwamnatin tarayya kan ta aiwatar da yarjejeniyoyin da aka yi a baya.

Dakta Suleiman ya ce yajin aikin ya zama dole ne bayan gwamantin ta kasa aiwatar da yarjejeniyar da ake da ita duk da tarurruka da roƙe-roƙe da gargaɗi da ƙungiyar ta yi.

“Buƙatunmu ba wai na son kai ne ko siyasa ba, muna neman yanayi mai kyau da zai bai wa likitoci damar yin aiki cikin aminci da kulawa da inganci ga marasa lafiya ba tare da hatsarin lafiyar su ba,” in ji shi.

Daga cikin manyan ƙorafe-ƙorafen NARD sun haɗa da albashin da ba a biyasu ba da rashin kyawawan yanayin aiki da ƙarancin ma’aikata, nauyin aiki mai yawa, da kuma rashin kayan aiki na asibiti, waɗanda ya ce sun lalata tsarin kiwon lafiya a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp