Home Labarai Likitoci masu neman ƙwarewa na yajin aiki a Najeriya

Likitoci masu neman ƙwarewa na yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa Najeriya (NARD) sun fara yajin aiki na dindindin daga ranar Asabar, lamarin da ya tsayar da ayyuka da dama a cibiyoyin kiwon lafiya a faɗin ƙasar.

Shugaban NARD, Dakta Mohammad Suleiman, ya tabbatar da fara yajin aikin a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar.

Wannan yajin aiki na zuwa ne bayan cikar wa’adin kwanaki 30 da ƙungiyar ta bai wa gwamnatin tarayya kan ta aiwatar da yarjejeniyoyin da aka yi a baya.

Dakta Suleiman ya ce yajin aikin ya zama dole ne bayan gwamantin ta kasa aiwatar da yarjejeniyar da ake da ita duk da tarurruka da roƙe-roƙe da gargaɗi da ƙungiyar ta yi.

“Buƙatunmu ba wai na son kai ne ko siyasa ba, muna neman yanayi mai kyau da zai bai wa likitoci damar yin aiki cikin aminci da kulawa da inganci ga marasa lafiya ba tare da hatsarin lafiyar su ba,” in ji shi.

Daga cikin manyan ƙorafe-ƙorafen NARD sun haɗa da albashin da ba a biyasu ba da rashin kyawawan yanayin aiki da ƙarancin ma’aikata, nauyin aiki mai yawa, da kuma rashin kayan aiki na asibiti, waɗanda ya ce sun lalata tsarin kiwon lafiya a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp