Gwamnatin Najeriya ta ce za ta yi maraba da duk wani taimako daga Amurka kan magance masatsalar masu tayar da ƙayar baya, matsawar za a mutunta kimarta.
Mai magana da yawon shugaban ƙasar, Daniel Bwala ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi ya ce kamat yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito”Muna maraba da taimakaon Amurka wajen yaƙi da masu tayar da ƙaya baya a ƙasarmu matsawar za ta kare mutuncinmu”.
Read Also:
Shugaba Trump na Amurka ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya, idan hukumomin ƙasar ba su ɗauki mataki bakan abin da ya kira ”yi wa kiristoci kisan kiyashi a ƙasar”.
A ranar Lahadi ne Donald Trump ya shaida wa manema labarai cewa sojojin Amurka za su aika dakaru Najeriya ko su ƙaddamar da hare-hare ta sama domin dakatar da abin da ya kira ”kisan kiristoci a ƙasar”, sai dai bai bayar da cikakken bayani ba.












