Home Bincike Bincike: Shin da gaske ne wata matashiya na fuskantar hukuncin kisa a...

Bincike: Shin da gaske ne wata matashiya na fuskantar hukuncin kisa a Jihar Zamfara Saboda Ta Sauya Addini zuwa Kiristanci?

Ikirari: Wani rubutu da ya karade kafafen sada zumunta na zamani da kuma wasu rahotannin kafafen yada labarai sun yi ikirarin cewa wata mata mai kimanin shekaru 22 a duniya mai suna Zainab Muhamadu na fuskantar hukuncin kisa a jihar Zamfara, bisa zargin sauya addininta daga Musulunci zuwa Kiristanci.

Rahotanni sun ce wani mai hidimar ƙasa (NYSC) da aka ce ana kiransa Fasto Samuel, ya rinjayi Zainab ta sauya addininta bayan sun kulla dangantaka ta ruhi da juna.

Jaridar The Guardian ta wallafa labarin da taken: “Zamfara Woman Faces Death Penalty for Converting to Christianity.” Wato wata ‘yar Zamfara na fuskantar hukuncin kisa bisa Sauya Addini.

Lamarin ya jawo cece-kuce daga masana harkar shari’a da masu rajin kare hakkin ɗan adam, wadanda suka bayyana lamarin a matsayin take hakkin dan Adam, musamman na ‘yancin addini da kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Tabbatar da Sahihancin Ikirari: Domin tantance sahihancin ikirarin, PRNigeria ta duba rahotanni daga kafafen yada labarai masu inganci. Sai dai, bayan The Guardian, wasu ‘yan kafafen labarai ne kadai suka wallafa irin wannan labari, kuma daga bisani wasu ciki har da Sahara Reporters sun goge labarin, lamarin da sanya shakku kan gaskiyar lamarin.

Bincike ya kara bayyana cewa Gwamnatin Jihar Zamfara ta fitar da sanarwar karyata wannan rahoto. Bisa ga rahoton jaridar Politics Digest, wanda bai ma wallafa labarin ba, gwamnatin ta bayyana ikirarin a matsayin “ƙarya kuma mai ɗauke da ruɗani,” tana zargin masu yada labarin da ƙoƙarin tayar da rikicin addini.

Shaidu: PRNigeria ba ta samu wata shaida ta gaskiya da ke nuna cewa an kama ko ana shari’a da wata mai suna Zainab Muhamadu a gaban kotun Shari’a a Zamfara ba.

Har ila yau, hoton da aka haɗa da labarin da ke yawo an gano cewa na wata mata ce mai suna Aalia Reeves, wata ‘yar asalin Amurka wadda ke ƙirƙirar abubuwan da suka shafi Musulunci a kafar TikTok.

Aalia ba ta taɓa zuwa Najeriya ba, balle a ce tana da alaƙa da jihar Zamfara ko wani lamari na sauya addini.

A cikin bidiyonta na TikTok, Aalia ta yi bayani yadda kishinta da sadaukarwarta ga addinin Musulunci ya taimaka wajen kyautata fahimtar mahaifiyarta Kirista game da addinin.

Kammalawa: Duk da yaduwar wannan labari da kuma wallafa shi da wasu kafafen yada labarai, babu wata shaida mai tushe ko tabbatacciya da ke nuna cewa akwai wata Zainab Muhamadu da ake tuhuma ko shari’a da ita a jihar Zamfara saboda sauya addini.

Hakanan hoton da ke cikin rahoton ba na Zainab ba ne, sai dai an dauki hoton Aalia Reeves domin ƙarfafa ƙaryar labarin.

Hukunci: labarin na Ƙarya ne, Babu wata shaida da ke nuna cewa gwamnatin Jihar Zamfara ta gurfanar da wata Zainab Muhamadu bisa sauya addini. Wannan ikirari ba shi da tushe, balle makama ya ta’allaka ne da ƙarya da satar hoto. Don haka, ƙaryane.

Daga PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp