Home Bincike Bincike: Shin da gaske ne an fuskanci yana sanyi mai tsananin gaski...

Bincike: Shin da gaske ne an fuskanci yana sanyi mai tsananin gaski a garin Jos wanda har kankara ke zuba?

IKIRARI: wani faifen Bidiyo da aka yada a kafafen sada zumunta na zamani, wanda ke nuna wata mata da wani abu mai kama da dusar kankara ya ke kewaye da ita bawan zubar ta, bidiyon ya yi ikirarin cewa garin Jos ne, babban birnin jihar Filato, dake tarayya Nijeriya.

A jikin bindiyon an rubuta “Dusar Kankara a Jos, Jihar Filato. Yanayin sanyi (winter) a Nijeriya? ABIN MAMAKI! Sauyin yanayi gaskiya ne,” ana lakanta canjin yanayin yana aukuwa saboda sauyin yanayi.

A bidiyon, an ga matar mamakin yanayin na “dusar kankara”, tana kuma daga abun da ya yi kama da kankarar ga wadanda suka zagaye ta suna kallo, cikin su har da matuka Babura da suak taru a wajen.

Tabbatar da sahihanci: domin  tabbatar da sahihancin abin da ake ikirari akai PRNigeria ta bi diddigin bidiyon na asali, wanda aka yada shi a wajen 21 ga watan Afrilun 2025.

Dukka dai haka, PRNigeria ta bincika rahoton hasashen yanayi a birnin Jos da ga watan Afrilun 21 zawa 29 ga watan Afrilun 2025. Hasashen ya bayyana karara cewa yanayi ya kasance gajimare jifa-jifa bisa ga ma’aunin Celcious 240C zuwa 300C. babu wani rahoton da ya nuna akwai yanayin zubar dusar kankara a dukkan yanayin.

An sake fadada bincike da suka hadar da yin amfani da hanyar binciken sahihancin bidiyo, wanda kuma ya tabbatar da an wallafa bidiyon ne  a kasar Kamaru. An wallafa shi ne a shafin facebook na NexDim Empire, shafin da ke yada abubuwan da suka shafi nishadantar a kasar wanda ke da mabiya sama da dubu 234.

Wadanda ke bayyana ra’ayin su karkashin bidiyon wanda aka tabbatar da ‘yan asalin kamaru ne wadanda ke korafin cewa dusar kankara ta lalata musu amfanin gona, har wani da ake kira da Terry Mcberi yak e cewa:

“dusar kankarar da ke zuba ta lalata mana amfanin gona amma mutane suna farin ciki, dan kankanin lokaci ya rage sai su ce basa jin dadin lokacin noma.

Wasu zababbun kalmomi da PRNigeria ta yi amfani da su sa ta tabbatar da yankin a kasar kamaru yake da ake kira da Aba Banki Tungoh wanda a arewa maso yammacin kasar yake, yankin da suke amfani da harshen Ingilishi.

Tarihin Zubar Dusar Kankara

Akwai karancin zubar dusar kankara sosai a yankin dake da yanayin zafi, sun taba samun rahoton samun zubar dusar kankarar kadan. Wanda an samu a a watan Disambar shekarar 1991, yayin da dusar kankarar ta zuba a wasu yankunan.

Kammalawa: binciken da PRNigeria ta gano wanda asalinsa ya fito ne da kasar Kamaru a yankin Aba Banki Tungoh, ba a garin Jos da ke Nijeriya ba.

Ikirarin da ake kan cewa an sami zubar dusar kankara a garin Jos ba gaskiya bane.

HukunciPRNigeria ta yanke hukunci kan wannan ikirari da ke cewa an sami zubar dusar kankarar  a garin Jos, saboda sauyon yanayin labara ne na Karya

PRNigeria

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp