Home General Wuta ta tashi a rumbun makamai na barikin sojoji a Maiduguri

Wuta ta tashi a rumbun makamai na barikin sojoji a Maiduguri

Hukumomi a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya sun tabbatar da tashin gobara a rumbun adana makamai da ke barikin sojoji da ake kira ‘Giwa Barrack’ a birnin Maiduguri.

Gobarar ta janyo fashewar abubuwa tare da haddasa fargaba a tsakanin al’umma a Maiduguri saboda ƙara mai ƙarfin gaske da aka ji a ƙwaryar birnin da kewaye.

Mazauna birnin Maiduguri sun shiga zulumi sakamakon tashin gobarar, inda galibin jama’a suka zaci cewa ‘yan Boko Haram ne suka kai hari.

Hukumar da ke kula da kashe gobara ta jihar Borno a cikin wata sanarwa, ta ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 10 da rabi na dare a ranar Laraba, inda ta lalata rumbun adana makamai na barikin sojojin.

Daga bisani ‘yan kwana-kwana sun samu nasarar kashe gobarar.

Binciken farko da hukumomi suka yi kan musababbin tashin gobarar, ya gano cewa tsananin zafi a Maiduguri na da alaƙa da tashin gobarar.

A shekara ta 2014 ne, ƙungiyar Boko Haram ta kai hari a barikin sojoji na Giwa lamarin da ya janyo hasarar rayuwa da dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp