Home General Wuta ta tashi a rumbun makamai na barikin sojoji a Maiduguri

Wuta ta tashi a rumbun makamai na barikin sojoji a Maiduguri

Hukumomi a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya sun tabbatar da tashin gobara a rumbun adana makamai da ke barikin sojoji da ake kira ‘Giwa Barrack’ a birnin Maiduguri.

Gobarar ta janyo fashewar abubuwa tare da haddasa fargaba a tsakanin al’umma a Maiduguri saboda ƙara mai ƙarfin gaske da aka ji a ƙwaryar birnin da kewaye.

Mazauna birnin Maiduguri sun shiga zulumi sakamakon tashin gobarar, inda galibin jama’a suka zaci cewa ‘yan Boko Haram ne suka kai hari.

Hukumar da ke kula da kashe gobara ta jihar Borno a cikin wata sanarwa, ta ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 10 da rabi na dare a ranar Laraba, inda ta lalata rumbun adana makamai na barikin sojojin.

Daga bisani ‘yan kwana-kwana sun samu nasarar kashe gobarar.

Binciken farko da hukumomi suka yi kan musababbin tashin gobarar, ya gano cewa tsananin zafi a Maiduguri na da alaƙa da tashin gobarar.

A shekara ta 2014 ne, ƙungiyar Boko Haram ta kai hari a barikin sojoji na Giwa lamarin da ya janyo hasarar rayuwa da dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp