Home General Gwamnoni za su fitar da dabarun yaƙi da matsalar tsaro a Arewa...

Gwamnoni za su fitar da dabarun yaƙi da matsalar tsaro a Arewa Maso Gabashin Najeriya

Ƙungiyar gwamnonin Arewa Maso Gabashin Najeriya ta ce za ta yi amfani dabaru daban-daban ta ƙarfi da lalama wajen tunkarar matsalolin tsaro da suka addabi yankin.

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne cikin bayanin bayan taro da gwamnan Taraba Agbu Kefas ya karanta bayan kammala taronsu karo na 11 a Damuturun jihar Yobe.

Gwamnonin sun ce dole ne a kawo ƙarshen matsalar rashin ayyukan yi na matasa, rashin ilimi mai inganci, rashin ababen more rayuwa da kuma sauran matsalolin da ke da alaƙa da talauci idan har ana son kawar da matsalar tsaro.

Yayin da zauren ke jinjinawa gwamnatin tarayyar ƙasar kan ƙoƙarinta a yaƙi da matsalar, ya kuma nuna damuwa game dawowar ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan yankin, a don haka su ka yi kira da jami’an tsaro da shugabannin al’umma su sake nazari kan dabarun yaƙi da matsalar.

Gwamnonin sun kuma nuna damuwa kan lalacewar manyan titunan ƙasar, wanda hakan ke ƙara ta’azzara matsalar tsaro da taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

Ƙungiyar ta kuma ƙudiri aniyar ƙarfafa dangantakar mambobinta domin bunƙasa harkokin noma, makamashi, bayar da horo domin rage rashin aikin yi na matasa, da kuma tunkarar matsalolin sauyin yanayi.

Taron wanda gwamnan Borno kuma shugabansa Babagana Zulum ya jagoranta, ya samu halartar gwamnonin Adamawa, Borno, Gombe, Taraba da Yobe, yayin da na Bauchi mataimakinsa ya wakilce shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp