Home General Gwamnoni za su fitar da dabarun yaƙi da matsalar tsaro a Arewa...

Gwamnoni za su fitar da dabarun yaƙi da matsalar tsaro a Arewa Maso Gabashin Najeriya

Ƙungiyar gwamnonin Arewa Maso Gabashin Najeriya ta ce za ta yi amfani dabaru daban-daban ta ƙarfi da lalama wajen tunkarar matsalolin tsaro da suka addabi yankin.

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne cikin bayanin bayan taro da gwamnan Taraba Agbu Kefas ya karanta bayan kammala taronsu karo na 11 a Damuturun jihar Yobe.

Gwamnonin sun ce dole ne a kawo ƙarshen matsalar rashin ayyukan yi na matasa, rashin ilimi mai inganci, rashin ababen more rayuwa da kuma sauran matsalolin da ke da alaƙa da talauci idan har ana son kawar da matsalar tsaro.

Yayin da zauren ke jinjinawa gwamnatin tarayyar ƙasar kan ƙoƙarinta a yaƙi da matsalar, ya kuma nuna damuwa game dawowar ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan yankin, a don haka su ka yi kira da jami’an tsaro da shugabannin al’umma su sake nazari kan dabarun yaƙi da matsalar.

Gwamnonin sun kuma nuna damuwa kan lalacewar manyan titunan ƙasar, wanda hakan ke ƙara ta’azzara matsalar tsaro da taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

Ƙungiyar ta kuma ƙudiri aniyar ƙarfafa dangantakar mambobinta domin bunƙasa harkokin noma, makamashi, bayar da horo domin rage rashin aikin yi na matasa, da kuma tunkarar matsalolin sauyin yanayi.

Taron wanda gwamnan Borno kuma shugabansa Babagana Zulum ya jagoranta, ya samu halartar gwamnonin Adamawa, Borno, Gombe, Taraba da Yobe, yayin da na Bauchi mataimakinsa ya wakilce shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp