Home General Gwamnoni za su fitar da dabarun yaƙi da matsalar tsaro a Arewa...

Gwamnoni za su fitar da dabarun yaƙi da matsalar tsaro a Arewa Maso Gabashin Najeriya

Ƙungiyar gwamnonin Arewa Maso Gabashin Najeriya ta ce za ta yi amfani dabaru daban-daban ta ƙarfi da lalama wajen tunkarar matsalolin tsaro da suka addabi yankin.

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne cikin bayanin bayan taro da gwamnan Taraba Agbu Kefas ya karanta bayan kammala taronsu karo na 11 a Damuturun jihar Yobe.

Gwamnonin sun ce dole ne a kawo ƙarshen matsalar rashin ayyukan yi na matasa, rashin ilimi mai inganci, rashin ababen more rayuwa da kuma sauran matsalolin da ke da alaƙa da talauci idan har ana son kawar da matsalar tsaro.

Yayin da zauren ke jinjinawa gwamnatin tarayyar ƙasar kan ƙoƙarinta a yaƙi da matsalar, ya kuma nuna damuwa game dawowar ayyukan ‘yan bindiga a wasu sassan yankin, a don haka su ka yi kira da jami’an tsaro da shugabannin al’umma su sake nazari kan dabarun yaƙi da matsalar.

Gwamnonin sun kuma nuna damuwa kan lalacewar manyan titunan ƙasar, wanda hakan ke ƙara ta’azzara matsalar tsaro da taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

Ƙungiyar ta kuma ƙudiri aniyar ƙarfafa dangantakar mambobinta domin bunƙasa harkokin noma, makamashi, bayar da horo domin rage rashin aikin yi na matasa, da kuma tunkarar matsalolin sauyin yanayi.

Taron wanda gwamnan Borno kuma shugabansa Babagana Zulum ya jagoranta, ya samu halartar gwamnonin Adamawa, Borno, Gombe, Taraba da Yobe, yayin da na Bauchi mataimakinsa ya wakilce shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp