Home General An naɗa sabon kwamandan da zai jagoranci yaƙi da Boko Haram a...

An naɗa sabon kwamandan da zai jagoranci yaƙi da Boko Haram a Najeriya

Rundunar sojojin Najeriya ta naɗa Manjo Janar Abdulsalam Abubakar a matsayin sabon kwamandan rundunar Operation Hadin Kai, wacce ke yaƙi da masu tada kayar baya a yankin arewa maso gabas ƙasar, bayan yawaitar kai hare-hare cikin watanni huɗu da suka gabata, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da sojoji da dama a yankin.

A cikin wata sanarwa da kakarin rundunar Reuben Kovangiya ya fitar, ta ce Janar Abubakar ne kwamandan rundunar na 15 da ke yaƙi da mayaƙa Boko Haram da kuma ISWAP a shiyar Arewa maso gabashin ƙasar.

A ƴan makonnin nan dai , mayaƙan Boko Haram da kuma ISWAP sun zafafa kai hare-hare a shiyar, lamarin da ya haifar da fargaba wajen sake dawowar mayaƙar masu iƙirarin jihadi, waɗanda ke amfani da ababen fashewa akan hanyoyi da dai-dai sauransu wajen kai hari.

Ko a jiya Talata sai da ƙungiyar ISWAP ta yi iƙirarin ɗaukar nauyin harin da aka kai jihar Borno da ya yi sanadiyar mutuwar mutum 26, ciki harda mata da ƙananan yara.

Sai dai sanarwar bata alaƙanta naɗin Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, da sabbin hare-haren da masu tada ƙayar bayan ke kaiwa a ƴan kwanakin nan ba.

Sama da shekara 15 ke nan sojojin Najeriya suka kwashe wajen yaƙi da masu tada ƙayar baya a shiyar Arewa maso gabashin ƙasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp