Home General An naɗa sabon kwamandan da zai jagoranci yaƙi da Boko Haram a...

An naɗa sabon kwamandan da zai jagoranci yaƙi da Boko Haram a Najeriya

Rundunar sojojin Najeriya ta naɗa Manjo Janar Abdulsalam Abubakar a matsayin sabon kwamandan rundunar Operation Hadin Kai, wacce ke yaƙi da masu tada kayar baya a yankin arewa maso gabas ƙasar, bayan yawaitar kai hare-hare cikin watanni huɗu da suka gabata, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da sojoji da dama a yankin.

A cikin wata sanarwa da kakarin rundunar Reuben Kovangiya ya fitar, ta ce Janar Abubakar ne kwamandan rundunar na 15 da ke yaƙi da mayaƙa Boko Haram da kuma ISWAP a shiyar Arewa maso gabashin ƙasar.

A ƴan makonnin nan dai , mayaƙan Boko Haram da kuma ISWAP sun zafafa kai hare-hare a shiyar, lamarin da ya haifar da fargaba wajen sake dawowar mayaƙar masu iƙirarin jihadi, waɗanda ke amfani da ababen fashewa akan hanyoyi da dai-dai sauransu wajen kai hari.

Ko a jiya Talata sai da ƙungiyar ISWAP ta yi iƙirarin ɗaukar nauyin harin da aka kai jihar Borno da ya yi sanadiyar mutuwar mutum 26, ciki harda mata da ƙananan yara.

Sai dai sanarwar bata alaƙanta naɗin Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, da sabbin hare-haren da masu tada ƙayar bayan ke kaiwa a ƴan kwanakin nan ba.

Sama da shekara 15 ke nan sojojin Najeriya suka kwashe wajen yaƙi da masu tada ƙayar baya a shiyar Arewa maso gabashin ƙasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp