Home General Aranposu ya bayar da tallafin magunguna ga hukumar KAROTA

Aranposu ya bayar da tallafin magunguna ga hukumar KAROTA

Mataimakain shugaban hukumar da ke lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano, KAROTA, Alhaji. Auwal Shuáibu Aranposu, ya bayar da tallafin maganguna ga asibitin hukumar domin inganta walwala da jin dadin ma’aikata.

Aranposu ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai, in da ya ce hakan na matsayin wani mataki na lura gami da inganta lafiyar jami’an hukumar, wadanda mafi yawan ayyukansu suna yi ne akan titinan jihar wajen dake da hadari.

Ya kuma kara da jan hankalin jami’an hukumar wajen kara lura a lokacin da suke tsaka da gudanar da aiki, sannan ya bukaci su da su yi amfani da asibitin yadda ya kamata.

Haka kuma ya bukaci malaman lafiyar da ke asibiti su yi amfani da magungunan yadda ya dace domin amfanin ma’aikatan hukumar.

Haka kuma ya kara tabbatarwa da jami’an irin yunkurin da hukumar ke yi waje ganin ta kare lafiya da rayukan dakarunta a dukkan in da suka sami kan su.

Daga bisani Aranposu ya yaba da kokarin jami’an wajen jajircewarsu a yayin da suke gudanar da ayyukansu, in da ya bukaci da su dore da hakan domin cigaban hukumar da jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp