Home General Aranposu ya bayar da tallafin magunguna ga hukumar KAROTA

Aranposu ya bayar da tallafin magunguna ga hukumar KAROTA

Mataimakain shugaban hukumar da ke lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano, KAROTA, Alhaji. Auwal Shuáibu Aranposu, ya bayar da tallafin maganguna ga asibitin hukumar domin inganta walwala da jin dadin ma’aikata.

Aranposu ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai, in da ya ce hakan na matsayin wani mataki na lura gami da inganta lafiyar jami’an hukumar, wadanda mafi yawan ayyukansu suna yi ne akan titinan jihar wajen dake da hadari.

Ya kuma kara da jan hankalin jami’an hukumar wajen kara lura a lokacin da suke tsaka da gudanar da aiki, sannan ya bukaci su da su yi amfani da asibitin yadda ya kamata.

Haka kuma ya bukaci malaman lafiyar da ke asibiti su yi amfani da magungunan yadda ya dace domin amfanin ma’aikatan hukumar.

Haka kuma ya kara tabbatarwa da jami’an irin yunkurin da hukumar ke yi waje ganin ta kare lafiya da rayukan dakarunta a dukkan in da suka sami kan su.

Daga bisani Aranposu ya yaba da kokarin jami’an wajen jajircewarsu a yayin da suke gudanar da ayyukansu, in da ya bukaci da su dore da hakan domin cigaban hukumar da jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp