Home General Aranposu ya bayar da tallafin magunguna ga hukumar KAROTA

Aranposu ya bayar da tallafin magunguna ga hukumar KAROTA

Mataimakain shugaban hukumar da ke lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano, KAROTA, Alhaji. Auwal Shuáibu Aranposu, ya bayar da tallafin maganguna ga asibitin hukumar domin inganta walwala da jin dadin ma’aikata.

Aranposu ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai, in da ya ce hakan na matsayin wani mataki na lura gami da inganta lafiyar jami’an hukumar, wadanda mafi yawan ayyukansu suna yi ne akan titinan jihar wajen dake da hadari.

Ya kuma kara da jan hankalin jami’an hukumar wajen kara lura a lokacin da suke tsaka da gudanar da aiki, sannan ya bukaci su da su yi amfani da asibitin yadda ya kamata.

Haka kuma ya bukaci malaman lafiyar da ke asibiti su yi amfani da magungunan yadda ya dace domin amfanin ma’aikatan hukumar.

Haka kuma ya kara tabbatarwa da jami’an irin yunkurin da hukumar ke yi waje ganin ta kare lafiya da rayukan dakarunta a dukkan in da suka sami kan su.

Daga bisani Aranposu ya yaba da kokarin jami’an wajen jajircewarsu a yayin da suke gudanar da ayyukansu, in da ya bukaci da su dore da hakan domin cigaban hukumar da jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp