Home Bincike Bincike: Shin da Gaskiya ne Gadar Sama da aka gidana kan Naira...

Bincike: Shin da Gaskiya ne Gadar Sama da aka gidana kan Naira Biliyan 10 a Lafia, dake jihar Nasarawa ta Rushe Bayan Mako Uku da Kaddamar da Ita?

Bincike: Shin da Gaskiya ne Gadar Sama da aka gidana kan Naira Biliyan 10 a Lafia, dake jihar Nasarawa ta Rushe Bayan Mako Uku da Kaddamar da Ita?

Ikirari: Wani hoto da ke yawo a shafukan sada zumunta kamar X (wanda aka fi sani da Twitter), Facebook da Instagram ya nuna cewa sabuwar gadar sama da aka kammala gina wa a Lafia, dake jihar Nasarawa, wadda aka kasha zunzurutun kudi har Naira biliyan 10 a kanta, ta rushe mako uku bayan kaddamar da ita.

Saƙon da ke tare da hoton yana cewa: “DA ƊUMI-ƊUMI: Gadar sama ta rushe bayan mako uku da kaddamar da ita a Lafia, Jihar Nasarawa. An kashe biliyan 10 a aikin. Nijeriya Kenan.”

Wannan ikirari ya jawo cece-kuce gami da nuna damuwa daga ‘yan Najeriya a shafukan sada zumunta, inda da dama ke kallon hakan a matsayin alamar cin hanci da rashin ingancin ayyukan gine-gine a ƙasar.

Lokacin da hoton ya bayyana da kuma tsananin mahawara da ake yi kan ingancin ayyuka a Nasarawa ya sa jama’a suka yi tunanin cewa gadar Lafia da aka kaddamar a watan Mayu 2025 da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya halarta, ta rushe.

Tabbatar da sahihancin Ikirari: Tawagar bincike ta PRNigeria ta gudanar da bincike mai zurfi don tabbatar da sahihancin ikirarin, inda ta gano cewa ikirarin ya fara yaduwa a ranar 23 ga Yuli, 2025.

Binciken ya gano cewa wannan ikirari ya fito ne bayan wani tabbataccen al’amari na rushewar wani sashi na gadar sama a Keffi, jihar Nasarawa. A ranar 18 ga Yuli, 2025, inda wata motar daukar kaya ta gugi  wani bangare na  turakun gadar, wanda hakan ya haifar da rushewar wani sashi na gadar, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum biyu da jikkatar wasu. A dalilin haka ne Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirin gyaran gaggawa na kwanaki 30 a wurin.

Wannan aikin da aka ce ya ci Naira biliyan 10 a zahiri ya ci Naira biliyan 16, kuma an kaddamar da shi ne a watan Mayu 2025, bisa halartar shugaba Tinubu da Gwamnan jihar Abdullahi Sule. Wadda ita ce gadar farko da aka gina a matsayin gada ta sama a birnin Lafia, kuma an kirkiro ta ne domin rage cunkoso da inganta zirga-zirgar ababen hawa a birnin.

Haka kuma, sakamakon bincike ta hanyar duba hoton da ake yadawa ya nuna cewa an taba amfani da shi a wasu lokuta daban-daban da ba su da alaka da Najeriya, ciki har da matsayin hoto na bogi da ke nuna wani bala’in gadar da aka ce ya faru a Bihar, India. Ko da yake an samu wani rushewar gada na gaske a Indiya a cikin wannan watan, amma ba shi ne hoton ba.

Nazarin hoto da kayan aikin tantance hotunan AI ya bayyana alamun karya kamar: karkacewar tsari, yanayin inuwa, da rashin cikar sifar mutanen dake hoton wadanda duk alamomi ne na hoton da aka kirkira da manhajar fasahar AI.

Kari a kan haka, babu wani rahoto daga kafafen yada labarai masu zaman kansu ko gwamnatin Nijeriya da ya tabbatar da wannan hoto ko faruwar lamarin.

Kammalawa: Binciken PRNigeria ya tabbatar da cewa babu wata hujja da ke nuna cewa gadar sama ta Lafia ta rushe. Hoton da ke yawo hoton kirkira ne da aka samar ta hanyar AI, kuma an taba amfani da shi a labaran ƙarya a wasu ƙasashe. Duk da cewa an samu wani rushewar gada na gaske a Keffi, babu abu da ya shafi gadar Lafia.

Hukunci: Labarin da ake yadawa KARYA NE

Hoton da ke yawo da ikirarin rushewar gadar sama a Lafia, jihar Nasarawa, karya ne kuma yana da niyyar yaudarar jama’a. Hoton na bogi ne da aka kirkira da fasahar AI.

Daga PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp