Home Labarai EFCC ta kama ƴan damfara ta intanet 25 a Jami’ar Bayero dake...

EFCC ta kama ƴan damfara ta intanet 25 a Jami’ar Bayero dake Kano

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya (EFCC) ta kama wasu mutum 25 da ake zargi da aikata damfara ta intanet a wani samame da ta kai a harabar jami’ar Bayero da ke Kano.

Hukumar ta ce jami’anta sun gudanar da samamen ne bisa sahihan bayanan sirri da suka samu da ke nuna cewa mutanen na da hannu a ayyukan damfara ta intanet da kuma satar bayanan mutane.

Hukumar ce ta sanar da hakan a shafin sada zumuntanta na X. inda ta ce dukkan waɗanda aka kama dalibai ne na jami’ar, kuma an gano wayoyi da kwamfutoci da mota kirar Honda Accord a hannunsu.

Kayan da aka kwato daga wurin sun haɗa da wayoyin salula, kwamfutoci, na’urorin haɗi da mota kirar Honda Accord.

EFCC ta ce an kama su ne bayan makonni ana sa ido a kansu kuma za a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp