Home Labarai NAFDAC ta gano gidan ajiye sinadaran haɗa abubuwa masu fashewa a Kano

NAFDAC ta gano gidan ajiye sinadaran haɗa abubuwa masu fashewa a Kano

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC) ta gano wani babban gidan ajiya a Kano da ke cike da sinadarai masu haɗari da ake amfani da su wajen haɗa abubuwa masu fashewa, ciki har da sinadarin sulphuric da nitric acid kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric acid da kuma lita 28,560 na nitric acid da kuma jarkoki da suka kai 330 da aka riga aka fitar da sinadaran cikinsu ba tare da sanin inda aka kai su ba a cikin gidan.

“Abin da muka gani a nan ya girgiza mu. Ban taɓa ganin adadin waɗannan sinadarai masu haɗari a wuri guda ba,” in ji Farfesa Adeyeye.

Hukumar ta ce ba a samu wandan yake da gidan ajiyar ba a lokacin da aka isa wurin, amma an kama wani ma’aikacin da ke kula da wurin, kuma ana ci gaba da bincike don gano wanda yake da wurin da kuma inda ya samo sinadaran da kuma inda yake kai su.

NAFDAC ta bayyana cewa sinadaran na cikin jerin kayan da ke da haɗari sosai ga mutane saboda haka sai da izini daga ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro kafin a shigo da su ƙasar.

Hukumar ta kuma tabbatar da cewa za ta lalata sinadaran bisa ka’idojin da suka dace don kare lafiyar jama’a, sannan za ta tabbatar da cewa an gurfanar da wanda ya mallaki sinadaran a gaban shari’a.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp