Home Labarai NAFDAC ta gano gidan ajiye sinadaran haɗa abubuwa masu fashewa a Kano

NAFDAC ta gano gidan ajiye sinadaran haɗa abubuwa masu fashewa a Kano

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC) ta gano wani babban gidan ajiya a Kano da ke cike da sinadarai masu haɗari da ake amfani da su wajen haɗa abubuwa masu fashewa, ciki har da sinadarin sulphuric da nitric acid kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric acid da kuma lita 28,560 na nitric acid da kuma jarkoki da suka kai 330 da aka riga aka fitar da sinadaran cikinsu ba tare da sanin inda aka kai su ba a cikin gidan.

“Abin da muka gani a nan ya girgiza mu. Ban taɓa ganin adadin waɗannan sinadarai masu haɗari a wuri guda ba,” in ji Farfesa Adeyeye.

Hukumar ta ce ba a samu wandan yake da gidan ajiyar ba a lokacin da aka isa wurin, amma an kama wani ma’aikacin da ke kula da wurin, kuma ana ci gaba da bincike don gano wanda yake da wurin da kuma inda ya samo sinadaran da kuma inda yake kai su.

NAFDAC ta bayyana cewa sinadaran na cikin jerin kayan da ke da haɗari sosai ga mutane saboda haka sai da izini daga ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro kafin a shigo da su ƙasar.

Hukumar ta kuma tabbatar da cewa za ta lalata sinadaran bisa ka’idojin da suka dace don kare lafiyar jama’a, sannan za ta tabbatar da cewa an gurfanar da wanda ya mallaki sinadaran a gaban shari’a.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp