Home General Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rasuwar Sarkin Gusau na jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rasuwar Sarkin Gusau na jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar sarki na 16 a jerin sakarakunan Gusau  mai Martaba Dr. Ibrahim Bello.

wannan dai na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Jihar Sulaiman Idris Ya fitar tare da bayyana jimamin Gwamnatin jihar bisa wannan babban rashi.

sanarwar ta kuma bayyana kaduwar gwamnan jihar Dauda lawan, wanda ya  bayyana marigayi sarkin matsayin babban uba kuma shugaba mai kishin ci gaban jihar Zamfara.

“Ina matuƙar alhini da jin labarin rasuwar mahaifinmu, Mai Martaba Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello.” in ji sanarwar.

“Ina mika ta’aziyya ta ga majalisar sarakunan jihar da iyalan marigayin da masarautar Gusau da kuma ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara.” gwamnan ya cewa.

Sarkin dai ya rasu a ranar Juma’a yana da shekaru 71, bayan fama da doguwar jinya a birnin Abuja, wanda shi ne sarki na 16 a jerin sarakunan Gusau, kuma ya gaji mahaifinsa da ya rasu a ranar 16 ga Maris, 2015.

Marigayin ya shafe shekaru 10 da wasu watanni yana kan karagar mulki. daga bisani sanarwa bayyana cewa za’a yi Jana’iza sa a yau juma a garin Gusua

Daga PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp