Home General Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rasuwar Sarkin Gusau na jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rasuwar Sarkin Gusau na jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar sarki na 16 a jerin sakarakunan Gusau  mai Martaba Dr. Ibrahim Bello.

wannan dai na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Jihar Sulaiman Idris Ya fitar tare da bayyana jimamin Gwamnatin jihar bisa wannan babban rashi.

sanarwar ta kuma bayyana kaduwar gwamnan jihar Dauda lawan, wanda ya  bayyana marigayi sarkin matsayin babban uba kuma shugaba mai kishin ci gaban jihar Zamfara.

“Ina matuƙar alhini da jin labarin rasuwar mahaifinmu, Mai Martaba Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello.” in ji sanarwar.

“Ina mika ta’aziyya ta ga majalisar sarakunan jihar da iyalan marigayin da masarautar Gusau da kuma ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara.” gwamnan ya cewa.

Sarkin dai ya rasu a ranar Juma’a yana da shekaru 71, bayan fama da doguwar jinya a birnin Abuja, wanda shi ne sarki na 16 a jerin sarakunan Gusau, kuma ya gaji mahaifinsa da ya rasu a ranar 16 ga Maris, 2015.

Marigayin ya shafe shekaru 10 da wasu watanni yana kan karagar mulki. daga bisani sanarwa bayyana cewa za’a yi Jana’iza sa a yau juma a garin Gusua

Daga PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp