Home Labarai Hare-haren ƴan bindiga a jihar Filato na ci gaba da lakume rayuka

Hare-haren ƴan bindiga a jihar Filato na ci gaba da lakume rayuka

Akalla mutum 14 da wani ɗan sanda na MOPOL ne suka mutu a hare-hare biyu da wasu ‘yan bindiga suka kai a ƙaramar hukumar Bokkos da ke Jihar Filato a ranar Alhamis, 24 ga Yuli, 2025.

Rahotanni sun ce an kai ɗaya daga cikin hare-haren ne da misalin ƙarfe 4 na yamma, yayin da mutanen da lamarin ya shafa mafi yawansu daga ƙauyen Chirang ke dawowa daga kasuwar Bokkos zuwa ƙauyen Mangor.

Shugaban masu sa ido kan zaman lafiya na ƙaramar hukumar Bokkos, Kefas Mallai ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga jaridar Punch inda ya ce mutane 14 ne suka mutu, yayin da wasu uku kuma suka jikkata.

A cewar Mallai, kafin wannan harin, wasu ‘yan bindiga sun harbe wani ɗan sandan MOPOL a wani shingen bincike da ke hanyar Richa a safiyar ranar.

Shugaban ƙaramar hukumar Bokkos, Amalau Amalau, ya bayyana lamarin a matsayin “taƙaici da ke buƙatar ɗaukar matakin gaggawa,” yana mai cewa an riga an kai gawarwaki da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Alabo Alfred, bai samu damar bayyana komai ba a lokacin da aka nemi jin ta bakinsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp