Home Labarai Yadda Hukumar KAROTA ta karbi koken direbobin mota a jihar Kano

Yadda Hukumar KAROTA ta karbi koken direbobin mota a jihar Kano

Wasu daga cikin Direbobin Bus a Jihar Kano sun koka bisa yadda Jami’an Hukumar Karota ke matsa mutsu Jahar.

Wannan na cikin wata sanarwa da Mai Magana da yawun hukumar ta KAROTA Abubakar Ibrahim Sharada ya fitar ya kuma aikewa manema labarai a jihar Kano.

Direbobin sun kai Koken ne a shalkwatar Hukumar ta lura da zirga-zirgar ababawan ta jihar Kano da nufin a duba domin magance masu matsalar.

Jagoran ayarin Kungiyar Matasan Direbobi ta Garin Kunya dake yankin Karamar Hukumar Minjibir, Mumfadalu Bukar Sakatare Ya koka bisa yadda jami’an Hukumar Karota Ke yawan kama Motocin Bus a duk lokacin da suka fito don gudanar da sana’ar su.

“Duk da cewar yanzu Direbobin a Daidaita Sahu sun Kwace mana akasarin Fasinjojin da mu direbobin Bus muke dauka hakan bata sanya Jami’an Karota sun saurara mana ba wajen kame Motocin mu”, inji Mumfadalu Sakatare.

“Tun da gwamatin Jahar Kano mai ci yanzu ta dagawa Direbobin A Daidaita Sahu kafa, to muma Direbobin Bus mun cancanci wani karamci na Gwamnati wajen karbar Kudaden shiga.” a cewar Jagoran Direbobin na Matasan Kunya.

Yana magane kan Kudaden Sticker wanda ya ce akan haka Jami’an Hukumar KAROTA Ke yawan kame motocin su.

A jawabin sa, Shugaban Hukumar KAROTA, Hon Faisal Mahmud Kabir ya yabawa Kungiyar Matasan Direbobi ta Garin Kunya bisa Kawo wannan koke da suka yi, a madadin sauran Direbobin Bus.

Manajan Daraktan wanda Daraktan kula da harkokin Kudaden shiga na Hukumar KAROTA, Alh Nura Ahmad Diso Ya wakilta yace abinda direbobin suka kawo koke akan sa hurumi ne na Gwamnatin Tarayya, don haka ya shawar ce su dasu miƙa Koken zuwa Hukumar tattara Kudaden Haraji ta Jahar Kano don magan ce al’amarin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp