Home Labarai Fadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu

Fadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso cewa gwamnatin Bola Tinubu ta watsar da yankin Arewa, tana mai cewa arewacin Najeriya na samun gagarumin kulawa a ayyukan ci gaba.
Kwankwaso, a wani taron tattaunawa kan gyaran kundin tsarin mulki da aka gudanar a Kano, ya soki gwamnatin Tinubu da karkatar da albarkatun ƙasa zuwa kudu, yana mai cewa hakan na ƙara jefa Arewa cikin fatara da rashin tsaro. Ya kuma koka da halin da titunan tarayya ke ciki a yankin, inda ya bada misalin wata tafiyarsa daga Abuja zuwa Kano da ya kira da “azaba” sakamakon lalacewar hanya.
Sai dai da yake mayar da martani, mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya ce kalaman Kwankwaso sun saba wa gaskiya, domin gwamnatin Tinubu na aiwatar da manyan ayyuka a Arewa da suka shafi hanyoyi, noma, lafiya da makamashi.
Ya lissafa muhimman ayyuka kamar titin Abuja–Kaduna–Kano, bututun iskar gas na Ajaokuta–Kaduna–Kano, shirin noma a jihohi tara, da aikin Kolmani a Bauchi da Gombe. Ya kuma ce an farfaɗo da cibiyoyin lafiya 1,000 a Arewa tare da bunƙasa wasu asibitoci manya.
Dare ya ƙara da cewa duk waɗannan nasarori an cimma su ne a cikin shekaru biyu kacal da Shugaba Tinubu ya hau mulki, yana mai cewa Arewa na da muhimmiyar matsayi a tsarin ci gaban gwamnatin.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp