Home Labarai Fadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu

Fadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso cewa gwamnatin Bola Tinubu ta watsar da yankin Arewa, tana mai cewa arewacin Najeriya na samun gagarumin kulawa a ayyukan ci gaba.
Kwankwaso, a wani taron tattaunawa kan gyaran kundin tsarin mulki da aka gudanar a Kano, ya soki gwamnatin Tinubu da karkatar da albarkatun ƙasa zuwa kudu, yana mai cewa hakan na ƙara jefa Arewa cikin fatara da rashin tsaro. Ya kuma koka da halin da titunan tarayya ke ciki a yankin, inda ya bada misalin wata tafiyarsa daga Abuja zuwa Kano da ya kira da “azaba” sakamakon lalacewar hanya.
Sai dai da yake mayar da martani, mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya ce kalaman Kwankwaso sun saba wa gaskiya, domin gwamnatin Tinubu na aiwatar da manyan ayyuka a Arewa da suka shafi hanyoyi, noma, lafiya da makamashi.
Ya lissafa muhimman ayyuka kamar titin Abuja–Kaduna–Kano, bututun iskar gas na Ajaokuta–Kaduna–Kano, shirin noma a jihohi tara, da aikin Kolmani a Bauchi da Gombe. Ya kuma ce an farfaɗo da cibiyoyin lafiya 1,000 a Arewa tare da bunƙasa wasu asibitoci manya.
Dare ya ƙara da cewa duk waɗannan nasarori an cimma su ne a cikin shekaru biyu kacal da Shugaba Tinubu ya hau mulki, yana mai cewa Arewa na da muhimmiyar matsayi a tsarin ci gaban gwamnatin.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp