Home Bincike Bincike: Shin da gaske ne ‘Yanbindiga sun mutu a yankin kabilar Nufawa...

Bincike: Shin da gaske ne ‘Yanbindiga sun mutu a yankin kabilar Nufawa bayan sun yi garkuwa da mutane?

Ikirari: Wani faifen bidiyo da aka yada ta manhajar whatsapp ya nuna wasu mutane kwance da bundugu raye a wuyansu. Wanda a jikin bidiyon aka rubuta cewa, wadannan wasu ‘yan bindiga ne da suka yi garkuwa da wasu mutane ‘yan kabilar Nufe a jihar Kwara, cikin garin Lafiagi, amma cuka mutu cikin sa’oi 24 da yin garuwar.

A jikin  bidiyo an yi rubutun ne kamar haka:

“Wannan lamarin ya auku ne a yankin al’ummar dake Magana da yaren Nufanci a jihar Kwara, a garin Lafiagi. An yi garkuwa da al’ummar yankin kuma aka kai su wani waje da babu wanda ya sani. Amma cikin sa’oi ashirin da hudu, kawai sai masu garkuwar suka fara mutuwa daya bayan daya, kamar yadda aka bayyana a bidiyon. A sama ga  gyarren bidiyon cikin harshen nufanci.”

A bidiyon, PRNigeria ta gano abinda ake cewa cikin harshen nufanci. Bayan ta fassara ana cewa wannan masu garkuwa ne bayan su yi garkuwa da mutane sun kai su daji, da safe, suka fara mutuwa daya bayan daya, ba tare da sanin makasudin hakan ba.

Mai maganar ya kara da cewa wadanda lamarin ya rutsa da su sun fantsama cikin daji domin tsira da rayukan, don haka ya kamata mutane su taya su murna domin “Allah ya fara amsar Addu’oin su.” Ya kuma yi addu’ar kada ‘yan ta’addan su sake zuwa garin Nufawa.

Binciken sahihancin labara: domin tabbatar da sahihancin ikirain, PRNigeria ta gudanar da bincike kwakkwafi kan bidiyon inda ta raba shi sala-sala a manhajar “Reverse image searches

Binciken ya nuna cewa hotunan dake cikin bidiyon ba daga jihar Kwara ya fito ba daga jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya yake.

Ya nuna mayakan Boko Haram ko ISWAP takwas da dakarun hadin gwiwa na CJTF da HF suka hallaka a garin Manawaji, dakekaramar hukumar Gamboru Ngala a jihar Borno. Sojojin sun sami nasarar hallaka mayakan bayan wani artabu da suka yi. Inda suka kwato makamai gami da alburusai.

Haka kuma wani bincike kan hotunan ya nuna shi matsayin hoton dake cikin hotunan da aka walafa a labarin nasarar da dakarun Operation Hadin kai suka samu a jihar Borno

Kammalawa: bidiyon dai na nuna hotunan mutum takwas na mayakan boko haram ko ISWAP da sojoji suka hallaka a jihar Borno bashi da wata alaka da jihar kwara.

Hukunci: ikirarin da ke cewa ‘yanbindiga sun mutum kwatsam a yankin da ake Magana da harshen Nufanci a jihar kwara bayan sun yi garkuwa da mazauna garin ba gaskiya bane, bidiyon da aka yi domin a karfafi hoton an yi shi ne da wata manufa

daga PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp