Home Labarai Ana fargabar mutuwar Mutane 16 sakamakon kifewar kwale-kwale a jihar Sokoto

Ana fargabar mutuwar Mutane 16 sakamakon kifewar kwale-kwale a jihar Sokoto

Akalla mutane  16 ne suka ake zargin sun mutu bayan wani kwale-kwale makre da mutane ya kife a jihar sokoto dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Dundaye inda hukumar agajin gaggauwa ta NEMA ta bayyana cewa akwai mutane 19 da suka tsira da rayukansu.

Kwale-kwalen na ɗauke da manoma ne inda zai kai su gonakinsu na shinkafa a ranar Lahadi.

An gano gawa guda, sannan kuma akwai mata da yara daga cikin waɗanda suka ɓace.

Masu ninƙaya da kuma masu kamun kifi na cikin waɗanda suka shiga aikin ceton.

Jami’ai sun ce jirgin ya ɗauko ninkin mutanen da ya kamata ya ɗauka ne.

A makon daya wuce ma wasu manoma 15 sun nitse bayan jirgin ruwan da ya ɗauko su ya kife a jihar Jigawa da ke arewacin Nijeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp