Home DUNIYA Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a jihar Filato

Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a jihar Filato

'Yan Ta'adda

Rahotanni daga jihar Filato na bayyana cewa wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun hallaka mutum biyar a karamar hukumar Bokkos na jihar.

Lamarin wanda ya faru a ranar Lahadi da daddare na zuwa ne kwanaki 11 bayan kai hari makamancinsa a karamar hukumar tare da kashe mutum bakwai.

an ruwaito cewa shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasum Fuddang, ya tabbatar da faruwar lamarin da kuma yin Alla-wadai da shi.

Ya ce an yi mutanen da aka kashen kwantan ɓauna lokacin da suke balaguro daga garin Mbar zuwa kauyen Koh na jihar.

Ƴan bindigar sun je ne a kan babura inda suka yi wa garin dirar mikiya da misalin karfe 7 na yammaci.

Fuddang ya soki jami’an tsaro saboda rashin mayar da martani a kan lokaci, inda ya ce kafin zuwarsu maharan sun riga da sun tsere.

Ya kuma nuna damuwar cewa irin waɗannan hare-hare da ake kai wa za su iya ɗaiɗaita al’ummomin yankin gabaki ɗaya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp