Home General kotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele Kyari

kotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele Kyari

Wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja babban birnin Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da wasu asusan da ke da alaƙa da tsohon shugaban kamfanin mai na NNPCL Mele Kyari.

Kotun ta bayar da umarnin dakatar da asusan na bankin Jaiz saboda zargin zamba da kuma halasta kuɗin haram.

Mai Shari’a Emeka Nwite ne ya bayar da umarni bayan wani lauyan hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci, Ogechi Ujam, ya nemi kotun ta dakatar da amfani da asusan har zuwa lokacin da hukumar za ta kammala bincike a kansu.

“Na saurari mai ƙorafi kuma na duba takardun ƙorafin da suka shigar masu ɗauke da hujjoji da bayanai. Na lura cewa buƙatarsu ta cancanci a amince da ita,” kamar yadda alƙalin ya bayyana.

Mai Shari’a Nwite ya ɗage sauraron batun har zuwa ranar 23 ga watan Satumba domin ganin rahoton binicken.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp