Home General Ana neman mutane 40 a cikin Kogi bayan kifewar kwale-kwale a Sokoto

Ana neman mutane 40 a cikin Kogi bayan kifewar kwale-kwale a Sokoto

Aƙalla mutum 40 ne ake nema bayan haɗarin kwale-kwale a ƙaramar hukumar Goronyo ta jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya a ranar Lahadi.

Tuni dai hukumar agajin gaggawa ta ƙasar tare da haɗin gwiwar hukumomin jihar suka bazama domin ceto waɗanda suka ɓacen.

Waɗanda lamarin ya shafa yawanci ƴan kasuwa ne da suke hanyar tafiya zuwa babbar kasuwar Goronyo da ke ci duk ranar Lahadi a lokacin da kwale-kwalen ya kife ɗauke da matafiya kusan 50, amma hukumomi sun ce an samu nasarar ceto mutum 10.

A mako uku da suka gabata ne aƙalla mutum 13 suka rasu bayan wani kwale-kwale ɗauke da mutum 100 ya kife a jihar Neja.

Haka kuma manoma 16 sun rasu wani haɗarin a watan Agustan 2024 a jihar ta Sokoto, sannan a ranar 29 ga watan Yuli, ƴanmata shida sun nutse bayan kwale-kwale ya kife da su a jihar Jigawa.

Ko a kwana biyun da suka gabata, wasu mutum 13 sun mutu a haɗarin kwale-kwale a jihar Neja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp