Home Labarai Hukumar KAROTA ta kaddamar da kotun tafi da gidanka a jihar Kano

Hukumar KAROTA ta kaddamar da kotun tafi da gidanka a jihar Kano

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano KAROTA ta kaddamar da kotunan tafi da gidanka a jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Abubakar Ibrahim Sharada Anipr ya aikewa PRNigeria, in da sanarwar ta ce hukumar ta dauki matakin ne don yankewa direbobi da ke karya dokar fitilun bada hannu a manyan titunan birni kano.

Da yake kaddamar da kotunan, Manajan Darakta na KAROTA, Hon. Faisal Mahmud Kabir, ya bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan umarnin da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bai wa hukumar domin tabbatar da bin dokokin zirga-zirga daga direbobi da masu tukin adaidaita sahu a jihar.

Manajan Daraktan ya jaddada cewa ganin yadda gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta zuba makudan kudade wajen girka sabbin fitilun hasken wuta masu amfani da rana (solar), dole ne masu ababen hawa su nuna godiya ta hanyar bin doka da odar.

ya kuma Ya ja kunnen duk direban da aka kama yana karya dokar cewar jami’an KAROTA tare da hadin gwiwar jami’an tsaro za su cafke shi domin a gudanar da shari’a nan take a gaban kotun tafi-da-gidanka.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp